Labarai
Za a samu jinkirin saukar damina a wasu jihohin Najeriya- Nimet
Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi hasashen cewa za a samu jinkirin saukar damina a wasu sassan ƙasar musamman jihohin yankin arewa ta tsakiya.
Ministan kula da harkokin sufurin jiragen sama da sararin samaniyar ƙasar, Festus Keyamo ne ya bayyana haka a lokacin fitar da rahoton hasashen da hukumar Nimet ta saba fitarwa na duk shekara.
Rahoton ya ce jihohin yankunan ƙasar da dama za su gamu da matsalar ɗaukewar damunar da wuri a bana.
Sai dai kuma hukumar ta NIMET ta ce, za kuma a samu saukar ruwan saman da wuri a jihohin Borno da Abiya da kuma Akwa Ibom saɓanin yadda aka saba gani.
Hasashen ya nuna cewa, za a samu ɗaukewar ruwan sama da wuri a jihohin Kano da Jigawa da Sokoto da Kebbi da kuma Kaduna a yankin arewa maso yamma.
Sai kuma Bauchi da Gombe da Yobe da Taraba a yankin Arewa maso gabas. Akwai kuma Filato da Nasarawa a yankin arewa maso tsakiya.
Sannan jihohin Legas da Ogun a kudu maso yamma da kuma Cross River a kudu maso kudu, da Ebonyi a kudu masu gabashin Najeriyar.
Sai dai kuma hasashen hukumar kula da yanayin ta Najeriya , NIMET ya nuna cewa wasu jihohin kasar za su iya samun saukar damina kamar yadda suka saba gani inda kuma za su samu ruwan sama kaman yadda suka saba samu a shekara.
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana