Connect with us

Labarai

Za a samu jinkirin saukar damina a wasu jihohin Najeriya- Nimet

Published

on

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi hasashen cewa za a samu jinkirin saukar damina a wasu sassan ƙasar musamman jihohin yankin arewa ta tsakiya.

Ministan kula da harkokin sufurin jiragen sama da sararin samaniyar ƙasar, Festus Keyamo ne ya bayyana haka a lokacin fitar da rahoton hasashen da hukumar Nimet ta saba fitarwa na duk shekara.

Rahoton ya ce jihohin yankunan ƙasar da dama za su gamu da matsalar ɗaukewar damunar da wuri a bana.

Sai dai kuma hukumar ta NIMET ta ce, za kuma a samu saukar ruwan saman da wuri a jihohin Borno da Abiya da kuma Akwa Ibom saɓanin yadda aka saba gani.

Hasashen ya nuna cewa, za a samu ɗaukewar ruwan sama da wuri a jihohin Kano da Jigawa da Sokoto da Kebbi da kuma Kaduna a yankin arewa maso yamma.

Sai kuma Bauchi da Gombe da Yobe da Taraba a yankin Arewa maso gabas. Akwai kuma Filato da Nasarawa a yankin arewa maso tsakiya.

Sannan jihohin Legas da Ogun a kudu maso yamma da kuma Cross River a kudu maso kudu, da Ebonyi a kudu masu gabashin Najeriyar.

Sai dai kuma hasashen hukumar kula da yanayin ta Najeriya , NIMET ya nuna cewa wasu jihohin kasar za su iya samun saukar damina kamar yadda suka saba gani inda kuma za su samu ruwan sama kaman yadda suka saba samu a shekara.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai14 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai15 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai16 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi17 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara