Connect with us

Fasaha

Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano

Published

on

 

 

Mazauna kauyen Yar’Gwanda dake karamar hukumar Tsanyawa ta Kano suna zaman jimami sakamakon rasuwar wani tsoho mai shekaru 60 mai suna Malam Danjuma da dansa Ibrahim mai shekaru 35 da haihuwa da kuma abokinsa Aminu Gaye da suka mutu a salga ko makewayi a kokarin cire wata wayar salula da ta fada a Masai irin na gargajioyar nan.

 

 

Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano Saminu Yusif Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin.

 

 

Ya bayyana cewa hukumar ta samu kiran gaggawa daga tashar kashe gobara ta Tsanyawa cewa wasu mutane hudu sun makale a a salga ko masai na gargajiya a lokacin da suke kokarin dauko wayar salular da ta fada.

 

 

Ya kuma jaddada cewa, nan take aka tura tawagar ceto zuwa wurin inda aka gano cewa Danjuma ya yi kokarin dauko wayarsa da ta fada cikin bandakin, inda ya makale. Bayan haka, dansa ya shiga bandaki don ya ceci mahaifinsa shi ma shiru sai abokinasa Gaye da Alasan suma sun shiga ne domin ceto mutanen biyu kuma suma suka makale.”

 

 

Saminu ya bayyana cewa, an ceto mutanen 3 na farko a sume yayin da na hudun na raye.

 

 

Jami’in hulda da jama’a ya ce rundunar ‘yan sandan ta kai wadanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibitin musamman na Bichi inda likitocin da ke bakin aiki suka tabbatar da mutuwar mutane ukun yayin da na hudun mai suna Abba Alhassan mai shekaru 28 a duniya yana samun kulawar likitoci.

 

Ya ce an mika wadanda suka mutun ne ga baturen ‘yansandan Tsanyawa Iro Lado.

 

 

Saminu ya bukaci jama’a da su daina jefa kansu cikin hadari, ya kuma shawarce su da su kai rahoton faruwar gobara, nutsewa, rugujewar gine-gine, da hadurran mota da dai sauransu zuwa ofishin hukumar kashe gobara mafi kusa da su ko kuma ta lambobin wayarsu na dake aiki ba dare ba rana.

 

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Ilimi2 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai2 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai4 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai4 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai6 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha7 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci7 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi7 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai1 week ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Mafi Shahara