Kasuwanci
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dakatar Da Yanka Nama A Mahauta Na Kwanaki 3
Gwamnatin jihar Kwara ta binne duk wani naman dabbobin da ake zargi yana dauke da guba don gujewa sayarwa mutane a kusa da Kwalejin Kolejin Koyon Larabci da Shari’ar Musulunci ta Jihar Kwara (CAILS) da ke Ilorin.
Hakan ya biyo bayan wasu matakan da aka dauka na hana mutane cin naman dabbobin da ake zargin yana dauke da guba a jihar.
A cikin wata sanarwa da babbar sakatariyar ma’aikatar noma da raya karkara, Madam Funke Sokoya ta fitar, ta ce gwamnatin jihar tare da hadin gwiwar sauran masu ruwa da tsaki sun amince da dakatar da ayyukan yanka dabbobi har na tsawon kwanaki uku domin a samu damar yin feshin magani a Mahautar don dakile duk wata cuta da ke gurin.
Sanarwar ta ce binciken farko ya nuna cewa mummunan lamarin ya faru ne sakamakon kiwo da gurbatacciyar ciyawa da ke kewaye da yankin.
Sanarwar ta bayyana cewa, ma’aikatar za ta kara sanya ido a sauran Mayanku daban-daban na jihar domin tabbatar da tsaftar muhalli.
A nasa jawabin, Daraktan Kula da Dabbobi, Dokta Olugbon Saliman, ya ce, za a rage yawan Mahauta da ba na gwamnati ba zuwa matakin da ma’aikatar za ta iya sarrafawa.
Ya ce duk wata Mayanka da ba ta bi ka’idojin gwamnati ba game da tsafta, za a rufe ta.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai7 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Fasaha7 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai4 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi2 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai2 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Labarai4 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas