Ilimi
Ƴan Sanda Za Su Yi Bincike Kan Makarantar Leads British
Rundunar ƴan sanda a babban birnin tarayya Abuja ta ce ta aika tawagar jami’anta zuwa makarantar Leads British bayan bidiyon yadda wata ɗaliba ke cin zalin ƴar ajinsu ya bazu a shafukan sada zumunta.
Kakakin rundunar, SP Josephine Adeh ta ce rundunar ta san da abin da ya faru kuma tana ɗaukan mataki a kai.
A cewar kakakin, ƴan sandan da aka tura za su gudanar da bincike tare da hana karya doka da oda.
A ranar Litinin ne bidiyon da ke nuna yadda ake cin zalin wata ɗaliba ya karaɗe shafukan sada zumunta lamarin da ya fusata al’ummar kasan nan.
Tuni dai hukumar makarantar ta fitar da sanarwa inda ta nemi yafiyar al’umma da kuma iyayen ɗaliban makarantar sannan ta ce ta soma bincike kan lamarin.
-
Labarai7 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi2 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai2 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Labarai4 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas