Labarai
Jirgin Sama Ya Zame Daga Kan Titinsa A Legas
Fasinjojin sun tsallake rijiya da baya, bayan jirgin saman da suka hau ya shige cikin jeji da su a Jihar Legas.
A yayin da ake ruwan sama ne wani jirgin fasinja mallakin kamfanin Dana Air ya zame daga kan titinsa a filin jirgi na Murtala Muhammad da ke Legas, sannan ya ci kasa a cikin jeji.
Hakan ya sa fasinjojin ficewa cikin gaggawa don tsira da rayuwarsu da kuma guje wa abin da ka iya biyowa baya.
Bidiyon abin da ya faru da fasinjojin suka ɗauka bayan sun tsallake rijiya da baya ya nuna tayar gaban jirgin ta nutse a kasa a cikin ciyayi.
Zuwa lokacin hada wannan rahoti dai hukumomi ko kamfanin Dana Air ba su ce komai kan lamarin ba.
Haka zalika babu bayanin cewa wani ya samu rauni ko kuma asarar rai ba.
-
Labarai6 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Fasaha7 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai4 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci7 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi2 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Ilimi7 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai2 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya