Labarai
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas
An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon aka yi kamen a jami’ar Texas da ke Dallas.
Wata sanarwa daga jami’ar ta ce ƴan sandan sun je makarantar bayan da masu zanga-zangar suka fara kafa sansani a babbar hanyar shiga makarantar.
An ba su gargaɗi a rubuce kan cewa su bar wajen kafin ƴan sanda su kutsa kai tare da tarwatsa wajen.
Ya zuwa ƙarfe 5:00 agogon ƙasar (22:00 GMT) na ranar Laraba ƴan sanda sun ce sun kama mutum 17 kan laifin ƙetare iyaka.
Daga bisani kuma kafar yaɗa labarai ta CBS ta yi rahoton cewa mutum 21 aka kama inda ta ruwaito lauyoyin waɗanda aka tsare.
BBC
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana