Labarai
An Kama Matasa Uku Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Rundunar ƴan sanda a jihar Nasarawa ta cafke wasu matasa uku kan zarginsu da haɗa baki don yunƙurin yin garkuwa da kawun ɗaya daga cikinsu.
Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Rahman Nansel ya sanyawa hannu, waɗanda ake zargi sun yi barazanar sace mutumin idan ya ƙi biyansu kuɗin fansa.
Sanarwar ta ce fargabar kada a sace shi ta sa mutumin ya tanadi kuɗin da matasan suka buƙaci ya ba su, inda ya ajiye shi a wurin da suka nema daga nan kuma suka kwashi kuɗin tare da rabawa a tsakaninsu.
Waɗanda ake zargin sun amsa laifin da ake zarginsu da yi sannan sanarwar ta ce ana ƙoƙarin bankaɗo wanda ya tsere.
-
Labarai7 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Fasaha7 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai4 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi2 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai2 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Labarai4 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas