Labarai
Tinubu Ya Nemi Shugabannin Addini Su Daina La’antar Kasan Nan A Wa’azinsu
Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi kira ga malamai da shugabannin addini da su guji “ƙasƙantarwa da kuma la’antar ƙasar” a cikin wa’azi kuma huɗubobinsu.
Tinubu ya yi kiran ne ranar Alhamis yayin da yake buɗe-baki tare da sarakuna da kuma jagororin addinin Musulunci da na Kirista a fadar shugaban ƙasa, yana mai jaddada cewa wa’azin da suke yi yana da matuƙar tasiri a cigaban ƙasar.
“Kishin ƙasar nan yana hannunku. Ku yi mata addu’a, ku ilimantar da yaranmu. Huɗubar da muke yi a masallatai da coci-coci na da matuƙar muhimmanci,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa: “Kada ku la’anci ƙasarku…Idan shugaba ba mutumin kirki ba ne ku bari zaɓe ya zo ku sauya shi, amma kada ku la’anci ƙasar. Da ma an tsara shugabanci ne da nufin kawo sauyi.”
Sarkin Zazzau Nuhu Bamalli ne ya wakilci Mai Alfarma Sarkin Musulmi Abubakar Sa’ad III a taron, wanda ya samu halartar Sakataren Ƙungiyar Kiristoci ta CAN Samson Fatokun.
Shi ma Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya nemi malaman da su “dinga haɗa kan al’umma don guje wa rikicin ƙabilanci da na addini”.
-
Labarai7 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai12 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Labarai11 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Kasuwanci1 day ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati