Labarai
Kungiyar Marayu Ta Yi Kira Ga Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gina Wa Mata Cibiyar Koyan Sana’o’i.
Kungiyar Marayu ta Jam’iyyatu Tukaful Aytam ta yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna ta taimaka mata wajen gina cibiyar koyarda sana’o’i.
Shugabar kungiyar, Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta yi wannan kiran a wurin taron rabawa Marayu Kayayyaki da ya gudana a harabar ofishin kungiyar dake Barnawa Kaduna
Ta ce samarda cibiyar zai taimaka wajen samarwa mata da matasa hanyar sana’o’i domin su dogara da kansu.
Har ila yau, ta ce samarda cibiyar zai taimaka wajen kawarda ayyukan shaye-shaye a tsakanin matasa da kuma rage radadin talauci a tsakanin al’umar yankin.
Da take tsokaci a wurin taron, shugabar kungiyar Nisa’us Sunnah dake Barnawa Kaduna, Malama Amina Namadi tace Kungiyar Jam’iyyatu Tukaful Aytam ta kwashe shekaru 14 wajen ayyukan kulada marayu ta hanyar tara taro-sisi a tsakanin mambobinta.
Ta kara da cewa, a haka kungiyar ta dauki alhakin kulada marayu 10 tun suna kanana har suka kai wani mataki ta hanyar sanyasu a makaranta da ciyarda su da tufatarda su tareda koya musu sana’o’in hannu.
Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin Hauwa Usman da Usman Bala, sun godewa Kungiyar bisa wannan yunkuri, tareda addu’ar samun daukaka don kaiwa ga babban matsayi.
Kayayyakin da kungiyar ta raba su ne, kayan abinci da masarufi ga marayunta 12, sai kuma kayan Sallah ga sauran marayu maza da mata 60.
Khadija Kubau
-
Labarai22 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai22 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Labarai6 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Labarai2 days ago
An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas