Connect with us

Labarai

Jam’iyyatut Takaful Aytam Ta Ziyarci Marasa Lafiya A Asibiti Dake Kaduna 

Published

on

Kungiyar Jam’iyyatut Takaful Aytam dake Kaduna ta ba da gudunmuwar kuɗi ga marasa lafiya dake kwance a asibitin Yusuf Dantsoho dake Kaduna.

 

Shugabar kungiyar, Malama Rabi’atu Adam Isma’il wadda ta jagoranci wakilan kungiyar zuwa asibitin, tace, wannan wani bangare ne na ayyukanta, su taimakawa mabukata a lokacin wannan wata mai albarka na Ramadan.

Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta yi bayanin cewa, yana daga cikin koyarwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW a ziyarci mara lafiya da ciyarda marayu da marasa karfi a lokacin azumin watan Ramadan da sauran lokuta.

 

Ta yi nuni da cewa, ba gwamnati ko wasu kungiyoyin kasashen waje ke tallafawa kungiyar ba, suna samun kudadensu ne ta hanyar tara taro-sisi a tsakanin wakilan kungiyar da wasu daidaikun jama’a.

 

Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta ce, kungiyar, ta baiwa kusan kowane majinyaci naira dubu wanda babu yawa, sai dai zai taimaka ma marasa lafiyan wajen sayen magani ko kayan marmari.

 

Ta nemi ganin gwamnati da mawadata da kungiyoyi masu zaman kansu su tallafawa kungiyar domin ta yi abinda ya fi haka a gaba wajen yi wa al’uma hidima.

 

A nata tsokacin, mataimakiyar shugabar kungiyar, Malama Ruqayya Ahmad Bashir ta ce, wakilai da abokanan kungiyar ne suka yanke shawarar harhada dan abinda Allah Ya hore musu domin tallafawa marasa lafiyan dake kwance a asibiti.

 

Ta kara da cewa, sun baiwa marasa­ lafiyan gudunmuwar ne ta hanyar nuna soyayya da tausayi, ta yi musu addu’ar samun lafiya cikin gaggawa.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana, Saleh Muhammad da Fatima Umar sun yabawa jagororin kungiyar akan tallafin kudin, sun yi addu’ar Allah Ya sa ka musu da mafificin sakamako.

 

Kungiyar ta ziyarci babban dakin marasa lafiya da dakin masu karaya ko quna da kuma dakin masu hatsari.

 

Khadija Kubau

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai12 mins ago

Majalisar Dattawan ta Amince da Hukuncin Kisa ga Masu Safarar Kwaya

Majalisar dattawan Najeriya ta amince da ƙudurin dokar hukuncin kisa ga masu safarar miyagun ƙwayoyi a faɗin ƙasar, bayan ƙudurin...

Labarai32 mins ago

Kotu ta Bayar da Belin Hadi Sirika kan Naira Miliyan 100

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama na Nijeriya, Hadi Sirika ya musanta zargin aikata laifin almundahana da ya shafi kusan Naira...

Labarai1 day ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai1 day ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci2 days ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha2 days ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha2 days ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai6 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Mafi Shahara