Connect with us

Ilimi

Sasantawa ce Jigon Kowane Irin Zaman Lafiya – Dr Joseph

Published

on

Cibiyar tabbatar da zaman lafiya da sasantawa ta ce tana ganawa da manyan abokan hulda da masu ruwa da tsaki a duk fadin kasar a wani yunkuri na samar da zaman lafiya ba tare da nuna banbancin addini ko kabalancin ba.

 

Babban daraktan cibiyar, Dr. Joseph Ochogwu ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a jihar Sokoto.

 

Mista Joseph Ochogwu ya ce cibiyar da ke karkashin ma’aikatar harkokin waje ta tarayya a halin yanzu tana hada kungiyoyin farar hula, hukumomin tsaro, malamai, kungiyoyin addini a kokarinta na tattauna hanyoyin da ake bukata da kuma samar da hanyoyi domin samun dauwamammen zaman lafiya a kasa.

 

Shugaban ya ce an dauki matakin ne da nufin inganta fahimtar juna tsakanin jama’a da dukkan gwamnatocin jihohi da nufin samar da ribar dimokuradiyya don samun ci gaba mai dorewa.

 

Ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta bukaci goyon bayan jama’a domin ba gwamnati damar samar da manufofi da tsare-tsare da suka shafi ci gaban tattalin arziki da tsaro a kasar nan.

 

Mista Joseph Ochogwu ya kara da cewa, za a iya cimma hakan ta hanyar samar da zaman lafiya da sasanta rikici tsakanin gwamnatocin jihohi da al’ummomi a fadin kasar nan.

 

Ya kara da cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yana ajandar muhimman abubuwa guda takwas da suka ta’allaka gaba daya kan zaman lafiya, tsaro da ci gaban tattalin arziki.

 

NASIR MALALI/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Ilimi1 day ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai2 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai3 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai4 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai6 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha7 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci7 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi7 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai1 week ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Mafi Shahara