Ilimi
Sasantawa ce Jigon Kowane Irin Zaman Lafiya – Dr Joseph
Cibiyar tabbatar da zaman lafiya da sasantawa ta ce tana ganawa da manyan abokan hulda da masu ruwa da tsaki a duk fadin kasar a wani yunkuri na samar da zaman lafiya ba tare da nuna banbancin addini ko kabalancin ba.
Babban daraktan cibiyar, Dr. Joseph Ochogwu ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a jihar Sokoto.
Mista Joseph Ochogwu ya ce cibiyar da ke karkashin ma’aikatar harkokin waje ta tarayya a halin yanzu tana hada kungiyoyin farar hula, hukumomin tsaro, malamai, kungiyoyin addini a kokarinta na tattauna hanyoyin da ake bukata da kuma samar da hanyoyi domin samun dauwamammen zaman lafiya a kasa.
Shugaban ya ce an dauki matakin ne da nufin inganta fahimtar juna tsakanin jama’a da dukkan gwamnatocin jihohi da nufin samar da ribar dimokuradiyya don samun ci gaba mai dorewa.
Ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta bukaci goyon bayan jama’a domin ba gwamnati damar samar da manufofi da tsare-tsare da suka shafi ci gaban tattalin arziki da tsaro a kasar nan.
Mista Joseph Ochogwu ya kara da cewa, za a iya cimma hakan ta hanyar samar da zaman lafiya da sasanta rikici tsakanin gwamnatocin jihohi da al’ummomi a fadin kasar nan.
Ya kara da cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yana ajandar muhimman abubuwa guda takwas da suka ta’allaka gaba daya kan zaman lafiya, tsaro da ci gaban tattalin arziki.
NASIR MALALI/Wababe
-
Labarai6 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Fasaha7 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai4 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci7 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi1 day ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Ilimi7 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai2 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya