Kasuwanci
Tinubu Yayi Sabbin Nade-Nade A Kasuwar Shinko Ta Kasa
Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Mista Mairiga Aliyu Katuka a matsayin shugaban Hukumar kula da kasuwannin shinko na kasa.
Wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya fitar ta ce shugaban ya kuma nada Mista Emomotimi Agama a matsayin babban Darakta hukumar.
Frana Chukwuogor kuma an nada shi a matsayin Babban Kwamishinan kula da harkokin Shari’a.
Sai kuma Mista Bola Ajomale a matsayin Babban Kwamishinan kula da Ayyuka. Ita kuma Mrs. Samiya Hassan Usman a matsayin kwamishinar kula da harkokin hukumar.
Mista Lekan Belo kuwa a matsayin kwamishinan zartarwa. Da kuma Kasimu Garba Kurfi a matsayin Kwamishina.
Sanarwar ta kara da cewa, shugaba Tinibu ya bayyana kwarin gwiwar cewa dukkan mambobin hukumar za su yi amfani da kwarewarsu wajen ci gaba da aikin hukumar na samar da ingantacciyar kasuwa mai inganci, da gaskiya, ta yadda masu zuba jari za su samu kwarin gwiwa tare da bayar da gudummawa sosai ga harkokin kasuwanci. ci gaban tattalin arzikin kasa.
Bello Wakili/Wababe
-
Labarai6 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Fasaha7 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai4 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci7 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi2 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Ilimi7 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai2 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya