Labarai
ECOWAS Za Ta Kashe Dala Miliyan 25 Don Yaki Da Ta’addanci A Najeriya Da Nijar
Kungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma ECOWAS ta ware Dala miliyan 25 da zimmar yaƙi da ta’addanci a ƙasashen Najeriya, da Nijar, da Mali, da Burkina Faso.
Ecowas ta tsara kashe kuɗin ne a shekarar 2024, kamar yadda Kwamashinar Raya Al’umma ta ECOWAS Farfesa Fatou Sarr ta bayyana a hedikwatar ƙungiyar da ke Abuja yau Juma’a.
Farfesar ta ce an ware miliyan huɗu daga cikin kuɗin don ayyukan agaji musamman ga mutanen da bala’o’i suka shafa.
“Haka nan, ECOWAS ta ware dala miliyan ɗaya da zimmar daidaita rayuwar mutanen da ta’addanci ya shafa, kamar ‘yan gudun hijira da kuma waɗanda aka ji wa rauni,” inji ta.
Ta ƙara da cewa a 2023 kaɗai, ECOWAS ta ba da tallafin Dala miliyan goma sha biyu da dubu dari shida ga mutane sama da miliyan huɗu da ta’addanci ya shafa a yammacin Afirka.
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai3 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Labarai5 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas