Labarai
Shugaba Tinubu ya Ayyana Masu Garkuwa da Mutane a Matsayin Yan ta’adda
Shugaban Kasar Nijeriya Ahmed Bola Tinubu ya bayyana cewa ya zama dole a riƙa ɗaukan mutanen da ke da hannu a aikata miyagun laifuka a matsayin ƴan ta’adda.
Shugaban ya bayyana haka ne ranar Talata a taron buɗe-baki tare da ma’aikatan shari’a na gwamnatin tarayya bisa jagorancin alƙalin alƙalai na ƙasa, mai shari’a Olukayode Ariwoola.
Da yake nanata ƙudirin gwamnati na murƙushe ƴan bindiga, shugaba Tinubu ya ce waɗanda suke sace yara matsorata ne da ba za su iya gaba da gaba da sojojin Najeriya ba.
“Dole ne mu ayyana masu garkuwa a matsayin ƴan ta’adda,” in ji shugaban ƙasar, kamar yadda wata sanarwa da kakakinsa Ajuri Ngelale ta ruwaito.
Bello WAKILI
-
Labarai3 days ago
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
-
Kasuwanci4 days ago
CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101
-
Fasaha3 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa
-
Labarai5 days ago
An Kwashe Mutane Da Dama Bayan Mummunar Ambaliyar A China
-
Fasaha5 days ago
Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano
-
Ilimi7 days ago
Sasantawa ce Jigon Kowane Irin Zaman Lafiya – Dr Joseph
-
Labarai13 hours ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus