Fasaha
Za a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin Najeriya – Nimet
Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki matakan kare lafiya ba, to akwai yiyuwar mazauna Abuja, Kano, da sauran jihohin Arewa da dama za su fuskanci tsananin zafi wanda zai shafi lafiyarsu.
Tsananin zafi dai na janyo cutuka da dama waɗanda za su iya kai wa mutuwa, kuma hakan a faruwa ne a lokacin da jiki ya kasa sarrafa zafin.
Mazauna waɗannan jihohin na iya fuskantar matsanancin zafi, wanda zai sa su shiga yanayi mara kyau, a cewar Nimet.
“Mun sake shiga lokacin zafi. Ya kamata jama’a su ɗauki matakan da suka dace,” kamar yadda “NiMET ta yi gargaɗi.
Ta ce Abuja, Kano, Sokoto, da Kogi ne za su fi fuskantar tsananin zafi, inda ta shawarci mazauna yankunan da su ɗauki matakin kariya da ya kamata.
Wasu jihohin da ke cikin rukunin fuskantar zafin sun haɗa da Kebbi, Katsina, Adamawa, Gombe, Bauchi, Taraba, Neja, Zamfara, Nasarawa, Jigawa, Benue, da kuma Kwara.
NiMET ta kuma gargaɗi mazauna jihohin Osun, Ekiti, Ondo, Bayelsa, Akwa Ibom, Anambra, Delta, Enugu, Edo, Ogun, Plateau, Borno, Imo, Abia, da Cross River da cewa su kasance cikin shiri don karuwar zafi, duk da cewa zafin ba zai yi tsanani ba kamar na sauran jihohi.
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai10 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa