Kasuwanci
Kasashen Afirka Na Taro Kan Ta’addanci A Abuja
An buɗe taron yini biyu kan yaƙi da ta’addanci a ƙasashen Afirka da ke gudana a Abuja, babban birnin Najeriya.
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ne ya ƙaddamar da taron mai taken ‘ƙarfafa ayyukan haɗin kai tsakanin ƙasashe da bunƙasa hukumomi don murƙushe ta’addanci’.
An shirya taron domin ƙarfafa yaƙi da ta’addanci a tsakanin ƙasashen nahiyar Afirka ta hanyar haɗin kai na sojoji da daƙile kwararar makamai da kuɗade tsakanin ƙasashen da zummar tallafa wa masu aikata manyan laifuka.
Taron na zuwa ne yayin da ƙasashen Afirka da dama ke fuskantar barazanar tsaro daga ƙungiyoyin masu iƙirarhin jihadi da ƴan bindiga musamman a sassan yankin Sahel.
Shugabanin ƙasashe daga yankin da masana kan harkoki tsaro daga nahiyar da ɓangaren majalisar ɗinkin duniya ne za su halarci taron.
-
Labarai6 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Fasaha7 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai4 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci7 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi2 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Ilimi7 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai2 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya