Connect with us

Labarai

Kotu ta Tsare Mutum 29 da Ake Zargi da Fafutukar Kafa Kasar Yarabawa

Published

on

Kotun majistre ta Iyaganku da ke Ibadan ta bayar da umarnin a tsare mutum 29 da ake zargin masu fafutukar kafa ƙasar Yarabawa ne saboda yadda suka yi wa harabar sakatariyar jihar Oyo ƙawanya.

A ranar Laraba ne aka gurfanar da mutanen saboda zargin su da hannu a harim da suka kai kan sakatariyar da kuma ofishin gwamna da bai yi nasara ba.

A baya-bayan nan ne wasu mutane da suka rufe fuskarsu suka yi dirar mikiya a sakatariyar jihar inda suka kafa tutarsu kafin jami’an tsaro su tarwatsa su.

A cewar jaridar Vanguard, mutanen waɗanda ke fuskantar tuhume-tuhume bakwai kan haɗa baki da cin amanar ƙasa da kuma shiga haramtacciyar ƙungiya da riƙe makami cikin jama’a da kuma aikata abin da ka iya kawo barazana ga zaman lafiya da mallakar makami ba bisa ƙa’ida ba.

Mutanen da ake zargi, har da wata matashiya da manyan mata biyar, an tsare su a gidan gyaran hali da ke Ibadan bisa umarnin babban majistare, Olabisi Ogunkanmi.

Daga bisani kuma mai shari’ar ya ɗage sauraron ƙarar zuwa 1 ga watan Agusta.

Labarai

Labarai57 mins ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai2 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai5 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara