Labarai
Jiragen Soji Sun Kashe Kwamandojin ISWAP A Borno
Farmakin Rundunar Sojin Saman Najeriya a maboyar ‘yan ta’addar ISWAP ya hallaka sama da kwamandojin ‘yan bindiga 30 a kauyen Kolleram da ke gabar tafkin Chadi, a Jihar Borno.
Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar sojojin saman Najeriya, AVM Edward Gabkwet, ya sanar cewa daga cikin manyan kwamandojin ’yan ta’addan da aka kashe a harin akwai Ali Dawud da Bakura Fallujah da kuma Malam Ari.
Sanarwar da Gabkwet, ya fitar ranar Talata a Abuja ta ce jiragen yakin Operation Hadarin Kai na Sojin Saman Najeriya sun kai farmakin ne ranar Asabar 13 ga Afrilu.
Ya bayyana cewa, harin ya yi wa ’yan ta’addanci mummunan illa a yankin Arewa maso Gabas, wanda hakan wata garumar nasara ce ga yunkurin dakile ta’addanci a yankin.
“Bugu da kari, harin ya lalata motocin ’yan ta’adda da dama da babura, da kayayyakin amfaninsu, wanda hakan cikas ne ga ayyukan ‘yan ta’addan.
“Bayanan sirrin da aka tattara bayan harin saman sun nuna cewa bama-bamai da aka harba sun lalata wata cibiyar ’yan ta’adda da ke cikin yankin Kolleram, inda suke sarrafa abinci da sauran abubuwa.
“Nasarar wadannan hare-hare ta sama na kara jaddada kudurin Rundunar Sojin Najeriya na kawar da ta’addanci da kuma tabbatar da tsaron ’yan kasa.
“Aikin ya yi matukar nasarar rage karfin kungiyar ISWAP a yankin ta hanyar kawar da manyan ’yan ta’adda da lalata kayayyakin aikinsu.”
PR/Usman Sani./Wababe
-
Labarai2 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai5 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai4 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa