Connect with us

Labarai

Jiragen Soji Sun Kashe Kwamandojin ISWAP A Borno

Published

on

Farmakin Rundunar Sojin Saman Najeriya a maboyar ‘yan ta’addar ISWAP ya hallaka sama da kwamandojin ‘yan bindiga 30 a kauyen Kolleram da ke gabar tafkin Chadi, a Jihar Borno.

Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar sojojin saman Najeriya, AVM Edward Gabkwet, ya sanar cewa daga cikin manyan kwamandojin ’yan ta’addan da aka kashe a harin akwai Ali Dawud da Bakura Fallujah da kuma Malam Ari.

Sanarwar da Gabkwet, ya fitar ranar Talata a Abuja ta ce jiragen yakin Operation Hadarin Kai na Sojin Saman Najeriya sun kai farmakin ne ranar Asabar 13 ga Afrilu.

Ya bayyana cewa, harin ya yi wa ’yan ta’addanci mummunan illa a yankin Arewa maso Gabas, wanda hakan wata garumar nasara ce ga yunkurin dakile ta’addanci a yankin.

“Bugu da kari, harin ya lalata motocin ’yan ta’adda da dama da babura, da kayayyakin amfaninsu, wanda hakan cikas ne ga ayyukan ‘yan ta’addan.

“Bayanan sirrin da aka tattara bayan harin saman sun nuna cewa bama-bamai da aka harba sun lalata wata cibiyar ’yan ta’adda da ke cikin yankin Kolleram, inda suke sarrafa abinci da sauran abubuwa.

“Nasarar wadannan hare-hare ta sama na kara jaddada kudurin Rundunar Sojin Najeriya na kawar da ta’addanci da kuma tabbatar da tsaron ’yan kasa.

“Aikin ya yi matukar nasarar rage karfin kungiyar ISWAP a yankin ta hanyar kawar da manyan ’yan ta’adda da lalata kayayyakin aikinsu.”

PR/Usman Sani./Wababe

Labarai

Labarai4 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai2 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai5 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara