Connect with us

Labarai

Jiragen Soji Sun Kashe Kwamandojin ISWAP A Borno

Published

on

Farmakin Rundunar Sojin Saman Najeriya a maboyar ‘yan ta’addar ISWAP ya hallaka sama da kwamandojin ‘yan bindiga 30 a kauyen Kolleram da ke gabar tafkin Chadi, a Jihar Borno.

Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar sojojin saman Najeriya, AVM Edward Gabkwet, ya sanar cewa daga cikin manyan kwamandojin ’yan ta’addan da aka kashe a harin akwai Ali Dawud da Bakura Fallujah da kuma Malam Ari.

Sanarwar da Gabkwet, ya fitar ranar Talata a Abuja ta ce jiragen yakin Operation Hadarin Kai na Sojin Saman Najeriya sun kai farmakin ne ranar Asabar 13 ga Afrilu.

Ya bayyana cewa, harin ya yi wa ’yan ta’addanci mummunan illa a yankin Arewa maso Gabas, wanda hakan wata garumar nasara ce ga yunkurin dakile ta’addanci a yankin.

“Bugu da kari, harin ya lalata motocin ’yan ta’adda da dama da babura, da kayayyakin amfaninsu, wanda hakan cikas ne ga ayyukan ‘yan ta’addan.

“Bayanan sirrin da aka tattara bayan harin saman sun nuna cewa bama-bamai da aka harba sun lalata wata cibiyar ’yan ta’adda da ke cikin yankin Kolleram, inda suke sarrafa abinci da sauran abubuwa.

“Nasarar wadannan hare-hare ta sama na kara jaddada kudurin Rundunar Sojin Najeriya na kawar da ta’addanci da kuma tabbatar da tsaron ’yan kasa.

“Aikin ya yi matukar nasarar rage karfin kungiyar ISWAP a yankin ta hanyar kawar da manyan ’yan ta’adda da lalata kayayyakin aikinsu.”

PR/Usman Sani./Wababe

Labarai

Labarai19 hours ago

Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran

Iran da Amurka za su shiga zagaye na biyu na tattauna batun taƙaita shirin nukiliyar Tehran a yau Asabar. Masu...

Labarai19 hours ago

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima

Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga...

Kasuwanci20 hours ago

‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su, a...

Kasuwanci20 hours ago

Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bukaci Kiristoci da su yi tunani a kan darussa, muhimmaci, da kuma kyawawan dabi’u...

Kasuwanci20 hours ago

Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.

Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma...

Kasuwanci20 hours ago

Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da cewa za ta gudanar da atisayen harbe-harbe ga sabbin ‘yan sanda a karamar...

Labarai20 hours ago

Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka

    Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman...

Labarai1 day ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci

  Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare...

Fasaha2 days ago

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye...

Kasuwanci2 days ago

Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (NSCDC) reshen jihar Zamfara, ta tura jami’ai 415 a fadin jihar domin tabbatar da...

Mafi Shahara