Labarai
BIKIN KARAMAR SALLAH: NSCDC Ta Tura Jami’ai 3,200 a Kano.
Rundunar tsaron farin kaya ta Najeriya, reshen jihar Kano, ta kammala dukkan shirye-shiryen tsaro da suka dace domin gudanar da bukukuwan karamar Sallah lafiya a jihar.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SC Ibrahim Idris Abdullahi ya fitar, ya ce kwamandan jihar, Mohammed Lawal Falala, ya amince da tura jami’ai sama da dubu uku da dari biyu a fadin jihar.
Jami’an da aka zabo daga ofisoshi na yanki da ma’aikatun za suyi aiki a filayen Idi daban-daban, wuraren shakatawa da ke a fadin Kano.
Sanarwar ta tabbatar da an tsara tsaro tare da dakile yiwuwar karya doka da oda kafin bukukuwan Sallah da bayan bukukuwan Sallah.
Sannan hukumar ta gargadin ‘yan daba da bata gari da su nisanta kansu daga duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaman lafiyar al’umma.
Jami’an rundunar a kodayaushe suna nan a kasa kuma a shirye suke don murkushe duk wanda aka kama yana karya doka a jihar.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai15 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai2 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka