Labarai
Zamu Tabbatar Da Anyi Bukukuwan Sallah Lafiya A Kebbi – ‘CP Chris
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kebbi, Chris Aimionowane, ya umurci, jami’an ‘yan sanda su ci gaba da aikin su na tabbatar da tsaro kafin da kuma lokaci da bayan bukukuwan Sallaha karama da za a fara gobe laraba..
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar ya fitar, ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar yayin da yake taya al’ummar musulmin jihar murnar kammala azumin watan Ramadan na bana yana yi wa daukacin al’ummar musulmi barka da Sallah.
Sanarwar ta yi kira ga al’ummar jihar da su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwan domin yin tunani da kuma yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban jihar da kasa baki daya.
Haka kuma ta yi kira ga malaman addini da masu ibada da mazauna jihar da su ba ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a jihar domin an samar da isasshen tsaro domin tabbatar da gudanar da bukukuwan sallah a jihar cikin kwanciyar hankali.
Yayin da yake gargadin duk masu tayar da hankali da mugun nufi da wani yunkurin kawo cikas ga bikin da su kaurace wa jihar, ya kuma umarci mutanen jihar Kebbi na gari da su ci gaba da zaman lafiya tare da gudanar da bukukuwa cikin kwanciyar hankali da lumana.
PR/Abdullahi Tukur/Wababe
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai17 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai3 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka