Connect with us

Labarai

Zamu Tabbatar Da Anyi Bukukuwan Sallah Lafiya A Kebbi – ‘CP Chris

Published

on

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kebbi, Chris Aimionowane, ya umurci, jami’an ‘yan sanda su ci gaba da aikin su na tabbatar da tsaro kafin da kuma lokaci da bayan bukukuwan Sallaha karama da za a fara gobe laraba..

 

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar ya fitar, ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar yayin da yake taya al’ummar musulmin jihar murnar kammala azumin watan Ramadan na bana yana yi wa daukacin al’ummar musulmi barka da Sallah.

 

Sanarwar ta yi kira ga al’ummar jihar da su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwan domin yin tunani da kuma yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban jihar da kasa baki daya.

 

Haka kuma ta yi kira ga malaman addini da masu ibada da mazauna jihar da su ba ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a jihar domin an samar da isasshen tsaro domin tabbatar da gudanar da bukukuwan sallah a jihar cikin kwanciyar hankali.

 

Yayin da yake gargadin duk masu tayar da hankali da mugun nufi da wani yunkurin kawo cikas ga bikin da su kaurace wa jihar, ya kuma umarci mutanen jihar Kebbi na gari da su ci gaba da zaman lafiya tare da gudanar da bukukuwa cikin kwanciyar hankali da lumana.

 

 

PR/Abdullahi Tukur/Wababe

Labarai

Labarai3 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai4 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai17 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara