Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Published

on

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu.

Jakadan Qatar a Najeriya Dr.  Ali Bn Ghanem Al-Hajari, ya yi wannan alkawarin  a yayin bikin kaddamar da ginin sabuwar makarantar firamare a Maiduguri babban birnin jihar Borno.

Ya bayyana cewa ilimi na da matukar muhimmanci wajen farfado da jihar da rikuci ya daidaita.

Jakadan wanda ya kaddamar da ginin tare da gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya jaddada cewa  idan aka kammala  za a  samar da kayan aiki na zamani don baiwa marayu damar koyo a kyakkyawan yanayi.

Gwamnatin Qatar za ta bayar da muhimmin tallafi ga marayu kusan 1000 a jihar Borno, za mu kuma ba da muhimmanci ga shirin gwamnati na samar da ingantaccen yanayin koyo ga yaran da rikicin Boko Haram ya daidaita.” Inji Ghanem.

Tunda farko Ambasada Ali Bn Ghanem Al-Hajari da mukarrabansa sun kai ziyarar ban girma ga Gwamna Babagana Zulum a fadar gwamnati inda ya sake jaddada aniyar kasarsa na taimakawa jihar Borno.

Gwamna Zulum ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin Qatar bisa tallafin tare da ba da tabbacin samar da yanayi mai kyau don samun ilimi mai inganci.

A watan Janairun bana ne gwamnan ya aza harsashin ginin gidan marayu da kungiyar agaji ta Qatar Charity Organisation ta gina.

Jakadan ya samu rakiyar mataimakinsa, Mista Abdullah Hilal Alnuimi, da daraktan kungiyar agaji ta Qatar Hamdi Abdou.

 

Dauda Iliya

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Ilimi3 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai3 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai5 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai5 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai1 week ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha1 week ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci1 week ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi1 week ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai2 weeks ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Mafi Shahara