Ilimi
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu.
Jakadan Qatar a Najeriya Dr. Ali Bn Ghanem Al-Hajari, ya yi wannan alkawarin a yayin bikin kaddamar da ginin sabuwar makarantar firamare a Maiduguri babban birnin jihar Borno.
Ya bayyana cewa ilimi na da matukar muhimmanci wajen farfado da jihar da rikuci ya daidaita.
Jakadan wanda ya kaddamar da ginin tare da gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya jaddada cewa idan aka kammala za a samar da kayan aiki na zamani don baiwa marayu damar koyo a kyakkyawan yanayi.
“Gwamnatin Qatar za ta bayar da muhimmin tallafi ga marayu kusan 1000 a jihar Borno, za mu kuma ba da muhimmanci ga shirin gwamnati na samar da ingantaccen yanayin koyo ga yaran da rikicin Boko Haram ya daidaita.” Inji Ghanem.
Tunda farko Ambasada Ali Bn Ghanem Al-Hajari da mukarrabansa sun kai ziyarar ban girma ga Gwamna Babagana Zulum a fadar gwamnati inda ya sake jaddada aniyar kasarsa na taimakawa jihar Borno.
Gwamna Zulum ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin Qatar bisa tallafin tare da ba da tabbacin samar da yanayi mai kyau don samun ilimi mai inganci.
A watan Janairun bana ne gwamnan ya aza harsashin ginin gidan marayu da kungiyar agaji ta Qatar Charity Organisation ta gina.
Jakadan ya samu rakiyar mataimakinsa, Mista Abdullah Hilal Alnuimi, da daraktan kungiyar agaji ta Qatar Hamdi Abdou.
Dauda Iliya
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai3 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Labarai5 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas