Labarai
Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Abinci Ga Iyalai Dubu Dari
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya kaddamar da rabon kayan abinci ga iyalai musu rauni sama da dubu dari daya a kananan hukumomin Maiduguri da Jere.
An yi rabon ne da nufin rage wahalhalun tsadar kayan abinci da sauran muhimman kayayyakin amfanin yau da kullun.
A jawabinsa yayin kaddamar da rabon kayayyakin a cibiyar wasanni ta Maiduguri, Gwamna Zulum ya ce kowane gida zai sami buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 25 da buhun masara shi ma mai nauyin kilogiram 25.
Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa ta ba da fifiko ga jin dadi da walwalar jama’a, musamman wadanda rikicin Boko Haram ya shafa.
“Mun kaddamar da rabon kayan abinci ga magidanta dubu dari ne daga birnin Maiduguri da kewaye. Kowa a Najeriya ya san irin wahalhalun da mutane ke fuskanta dangane da karancin abinci,” In ji Zulum.
A cewar Gwamnan, za a raba kayayyakin ne ga masu karamin karfi a cikin al’umma domin rage radadin tsadar rayuwa da ake fuskanta.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa za a kara yawan rabon tallafin daga iyalai dubu dari zuwa sama da iyalai dubu dari biyu a kananan hukumomi bakwai dake kudancin jihar kafin karshen azumin watan Ramadan.
Ya kara da cewa, “Muddin ni ne gwamnan jihar Borno, za a ci gaba da rabon kayayyakin jin kai. Duk da haka, ina so in jaddada cewa yayin da ake ci gaba da rabon kayan abinci, za mu ci gaba da bada tallafi harkar kasuwanci da noma”.
Ya bukaci al’ummar jihar da su himmatu wajen aikin noma don bunkasa samar da abinci, tare da ba da tabbacin samar da karin ababen more rayuwa da suka hada da shiga motocin bas kyauta, da kayan aikin gona da tallafin kudi don farfado da tattalin arzikin jihar.
Daga Dauda Iliya
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai9 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha1 day ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Fasaha1 day ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Kasuwanci1 day ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Labarai6 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas