Connect with us

Labarai

Gwamnatin Borno Ta Samar Da Gidaje Sama Da 400 Ga ‘Yan Gudun Hijira A Dalori

Published

on

Gwamnatin Jihar Borno ta fara rabon gidaje 447 na sake tsugunar da ‘yan gudun hijira a yankin Dalori dake karamar hukumar Konduga a jihar.

 

Gwamna Babagana Zulum wanda ya kaddamar da atisayen, ya kuma raba kayan abinci da sauran kayayyakin masarufi ga iyalan da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu.

 

Ya ce an zabo wadanda suka ci gajiyar tallafin ne daga sansanin ‘yan gudun hijira da ke Kawar Maila, inda iyalai 197 suka sami gidaje, yayin da iyalai 250 daga sansanin Dalori suka amfana.

Ya ce an samar wa al’ummar da aka sake tsugunar da su asibiti da makaranta da  ruwan sha.

 

Gwamnan ya ba da tabbacin cewa gwamnatinsa za ta kuma samar da kayayyakin noma da  tallafa ga ‘yan kasuwa domin ‘yan gudun hijirar da suka dawo su samu saukin ababen more rayuwa.

 

“Kowanne daga cikin gidajen 447, wadanda  suka kunshi mutane kusan dubu biyu da dari biyar  sun sami kayan abinci, da  tabarmi, da barguna da tufafi.” In ji Gwamna Zulum.

 

Zulum ya kuma yi tsokaci kan shirin sake ginawa da kuma tsugunar da al’ummar Dalwa da Sandiya da ‘yan ta’addan Boko Haram suka raba da muhallansu a karamar hukumar Konduga.

 

Hakazalika, Gwamna Babagana Zulum ya kuma bayar da umarnin rufe dukkan sansanonin ‘yan gudun hijira da ba  hukuma  ta kafa su ba  a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

 

Ya ce ba za a ci gaba da ajiye mutane a sansanoni ba, yana mai jaddada cewa za a rufe dukkan sansanoni da ke Maiduguri kafin ranar 29 ga Mayun 2024.

 

“Muna so a sami kamulallun  mutane  a cikin al’ummoma daban-daban domin bayar da gudummawar ci gaban jihar, don haka za mu mayar da su gidajensu domin su ci gaba da gudanar da al’amuran su na yau da kullun”. Inji  shi.

 

Gwamnan ya bayyana cewa an rufe dukkanin sansanonin ‘yan gudun hijira da gwamnati ta kafa a birnin Maiduguri da kewaye tun shekarar da ta gabata.

 

Daga Dauda Iliya

1 Comment

1 Comment

  1. Haladu Abdullahi

    February 28, 2024 at 5:50 am

    MUNA YABAWA GOMNA BABAGANA BISA WANNAN GAGARUMI AIKI DA YAYI

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai4 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai5 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci1 day ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha1 day ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha1 day ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai1 day ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara