Kasuwanci
Gobara Ta Lakume Kayayyaki Na Miliyoyin Naira A Kano
Wata gobara da ta tashi da tsakar dare ta lalata sama da shaguna 50 da kadarori da kudin su ya kai naira miliyan 150 a kasuwar ‘yan katako da ke Rijiyar Lemuo a karamar hukumar Fagge ta Kano.
Da yake zantawa da manema labarai shugaban kasuwar Alhaji Mamuda Musa Abdullahi ya bayyana cewa gobarar ta tashi ne da misalin karfe daya na daren Lahadi.
Ya yi nuni da cewa, gobarar ta kona sama da shaguna 50 da ke dauke da katako, da kumfa, da injin fkujeruda kujeru da sauran kayayyakin aiki.
Alhaji Mamuda ya ce har yanzu ba a kai ga gano musabbabin faruwar lamarin ba.
Shugaban kasuwar ya yabawa hukumar kashe gobara ta jihar Kano bisa gaggauta daukar matakan dakile gobarar.
Ya kuma yi kira ga gwamnati da masu hannu da shuni da su tallafya’yan kasuwar da lamarin ya shafa.
Daga Khadijah Aliyu
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai1 day ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana