Labarai
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ado Gwanja
Wata Babbar Kotu a Jihar Kano, karkashin jagorancin Mai Sharia Aisha Mahmud, ta ba da umarnin kamo mawaki Ado Isa Gwanja.
Kotun ta kuma haramta wa mawakin yin waka har zuwa lokacin da ’yan sanda za su kammala bincike a kansa.
Wannan dai na zuwa ne bayan da Majalisar Malamai ta Jihar Kano, ta maka Ado Gwanja da wasu kara a kotu, kan amfani da kalaman da ba su dace ba a wakokinsu.
Aminiya ta tuntubi, shugaban Kungiyar Jarumai na Kannywood, Alhassan Kwalle, amma jarumin, ya ce ba shi da masaniya game da umarnin kotun na kamo Ado Gwanja.
Idan ba a manta ba a 2023, kotu ta gayyaci Ado Gwanja, Idirs mai wushirya, Murja Ibrahim Kunya, 442 da wasu bayan da wasu mazauna Kano suka maka su a kotu kan zargin bata tarbiyyar yara.
A baya-bayan nan, Hukumar Hisba ta jihar, ta kama tare da gurfanar da fitacciyar ’yar TikTok, Murja Ibrahim Kunya a kotun Musulunci da ke Unguwar PRP a jihar.
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana