Connect with us

Labarai

Kotu Ta Baiwa EFCC Umurnin Cigaba Da Tsare Emefiele

Published

on

Babbar kotu a Ikeja da ke jihar Legas ta bayar da umarnin ci gaba da tsare tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele.

Za a ci gaba da tsare Emefiele a hannun hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa arzikin kasa ofzagon ƙasa har zuwa ranar 11 ga watan Afrilu da kotu za ta yanke hukunci kan ba shi beli.

Tun farko da ya bayyana a kotun, tsohon gwamnan babban bankin Najeriyar ya musanta sabbin tuhume-tuhumen da ake masa na karya dokokin da suka shafi hada-hadar kuɗaɗen waje da hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa arzikin ƙasa take masa.

EFCC ta zargi Emefiele da ware wasu kuɗaɗen waje kusan dala biliyan biyu ba tare da bin ka’ida ba.

Wannan na cikin tuhume-tuhume 26 da ake masa a ƙarar da aka gabatar gaban babbar kotun da ke Ikeja.

Matakin ya ƙara ta’azzara taƙaddamar shari’a tsakanin EFCC da tsohon gwamnan babban bankin wanda kuma yake fuskantar tuhuma kan almundahana da rashawa da haɗa baki wajen aikata laifi a Abuja, babban birnin Najeriya.

Emefiele, wanda ya bayyana gaban babbar kotu a Legas karƙashin mai shari’a Rahman Oshodi, ya musanta aikata zarge-zargen da ake masa.

An karanto masa tuhume-tuhume 26 da ake masa da wanda ake kararsu tare Henry Omoile.

Dukkansu sun musanta zarge-zargen da ake masu.

Sun kuma nemi kotu ta bayar da su beli zuwa lokacin da za a saurari ƙara.

Lauyan Emefiele, Lebi Lawal ya ce ya kamata kotu ta duba matsayin wanda yake karewa.

A cewar lauyan, “tsawon shekara tara, Emefiele ne ma’aikacin banki na ɗaya a Najeriya.

Lauyan ya kuma roƙi kotu ta sake nazari kan ɗabi’un Emefiele tun bayan kama shi.

Bayan hawansa kan mulki ne, shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya dakatar da Emefiele daga shugabancin babban bankin ƙasar.

Makonni bayan dakatar da shi ne kuma aka kama shi tare da gurfanar da shi gaban shari’a a watan Nuwamba kan zarge-zargen almundahana.

Labarai

Labarai3 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai4 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai17 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara