Ilimi
Shugaban Kasa Na Yiwa Al’ummar Musulmi Barka Da Sallah
![](https://radionigeriakaduna.gov.ng/hausa/wp-content/uploads/2024/02/7f560422-acf8-4f77-934b-99f5bee2ff2b.jpg)
Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga daukacin ‘yan Najeriya da su hada kansu su dukufa wajen gina kasa mai inganci.
Shugaban ya yi wannan roko ne a lokacin da yake taya al’ummar musulmi murnar sallah karama wanda ke nuna karshen watan Ramadan, mai alfarma da ke jaddada cikakkiyar mika wuya ga Allah Madaukakin Sarki da kuma umurninsa na sadaukarwa da hidima ga bil’adama.
A cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Ajuri Ngelale ya fitar, an bayyana cewa shugaban ya yi addu’ar Allah ya karba addu’o’i da sadaukarwa kowa da kowa a wannan Ramadan
Shugaban ya kuma yi fatan za a yi koyo da darussan da aka samu a wannan wata mai albarka,.
Bello Wakili/Wababe
-
Labarai7 days ago
Al’ummar Kauru Na Cikin Zullumi Bayan Lalacewar Gadar Da Ta Hadasu Da sauran Al’ummomin Jihar Kaduna
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Harkar Noma A Yobe
-
Labarai2 days ago
Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
-
Kasuwanci4 days ago
An Shawarci Matasan Jihar Niger Su Guji Shiga Zanga-Zangar Babu Gaira Babu Dalili
-
Labarai4 days ago
Zanga Zanga: Gwamnati Ta Baiwa Matasa Tabbacin Daukan Bukatun Su Da Mahimmanci
-
Labarai3 days ago
‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Za Ta Samar Da Kananan Jiragen Ruwa A Kananan Hukumomi 3
-
Labarai4 days ago
Taurarin Finafinan Hausa Na Alhinin Rasuwar Sulaiman Alaka