Connect with us

Ilimi

Bukin Sallah: Mai Martaba Sarkin Kauru Ya Bukaci A Ba Mata Dama Su Nemi Ilimi

Published

on

Mai martaba Sarkin Kauru ta jihar Kaduna Alhaji Zakari Ya’u Usman ya bukaci jama’ ar yankin su hada kai suyi aiki tare don dakile matsalar tsaron da yankin ke fuskanta a yanzu.

A sakon sa na barka da sallah a fadarsa da ke Kauru, Mai Martaba Sarki ya nuna matukar famuwarsa akan matslaar masu garkuwa da mutane da ke kara habaka da satar amfani gona da wasu ayukkan badala a wannan yankin.

Alhaji Zakari Ya’u ya zayyano irin kalubalen da wannan matsalar ke haifarwa tsakanin al’umma tare da kira da kakkausar murya na a dauki matakin maganinta gaba daya.

Ya Kuma bayyana irin mahimmancin hadin kan al’umma akan wannan don kawo karshensa sannan ya umurci dukkanin masu rike da sarautu suyi aiki da mutanensu tare da jami’an tsaro don samo hanyar dikile wannan muguwar ta’ada.

Mai Martaba Ya’u na II yace akwai bukatar hada karfi da karfe wajen Kare rayuka da dukiyoyi da kuma fitar da al’umma daga wannan sabuwar matsala.

Bugu da kari Banda maganar tsaro, mai martaba ya kuma tabo tare da bayyana muhimmamcin kula da ilimin ‘ya’ya mata tare da Kiran a kara basu dama suje makaranta.

Sarkin Kauru Zakari Ya’u Usman II da Malam Yusuf Zubairu (Tambarin Kauru)

Sannan yayi bayanin cewa gudummuwar da ilini ke bayarwa wajen ba jama’a damar dogara DA Kai da Kuma habakar tattalin arzikin da ci gaba.

Sannam mai Martaban bai tsaya nan ba sai da kawo irin mahimmancin da zaman lafiya da kwanciyar hankali da samarawa mabanbantan al’umma don haka ya bukaci a hada kai ayi aikin bunkasa yankin Kauru.

Ya Kuma jawo hankalin al’ummarsa game da mahimmancin zuwa asibiti don duba lafiya.

Radio Nigeria kaduna ya bada labarin cewa sakon mai martaba na sallah karama ya nuna irin yunkurin da yake wajen maganin matsalolin da jama’ar masarautar ke fuskanta, inda ya bayyana aiki tare ta bangaren ilimi, zaman lafiya da harkokin kula da lafiya a matsayin jigon ci gaban da ake bukata.

Sakataren masarautar Kauru, Mal Muhammad Sani Suleiman, (Dan’s buran Kauru)

 

Hakama Sakataren masarautar Kauru Malam Muhammad Sani Suleiman (Dan Buran Kauru) ya mika sakonsa na taya murna ga mi martaba Sarki Kauru game da cikar sa shekara 3 akan mulki.

Sakon Dan Buran na Kauru ya nuna irin godiya da yadda tsarin shugabancin mai martaba da irin gudummuwar da ya ke bayarwa ga bunkasar al’ummar yankin a wadannan shekarun 3.

Yusuf Zubairu

Labarai

Labarai23 mins ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai13 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Mafi Shahara