Connect with us

Labarai

Mai Martaba Sarkin Kauru Ya Kara Ankarar Da Al’ummarsa Kan Matsalar Tsaro

Published

on

Mai martaba Sarkin Kauru a Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u na biyu, ya kara  fadakar da al’ummar masarautarsa game da matsalar tsaro, duba da yadda ake  samun yawaitar satar mutane da ayyukan ‘yan bindiga a jihar.

 

Mai Martaba Alhaji Zakari Ya’u II, wanda ya bayyana haka a wajen taron buda baki na watan Ramadan na shekara-shekara a fadarsa da ke Kauru, ya jaddada muhimmancin yin taka tsantsan da hadin gwiwa da jami’an tsaro domin yakar kalubalen tsaro da ake fuskanta.

 

Mai Martaba Sarkin Kauru Alhaji Zakari Ya’u II

 

Sarkin ya kuma jaddada hakkin da ya rataya a wuyan ‘yan kasa wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a tsakanin al’umma, tare da yin kira da a hada kai domin tunkarar wadannan matsalolin yadda ya kamata.

Ya kuma nanata kiransa na ci gaba da hada kai da jami’an tsaro,  yana mai karfafa gwiwar mazauna yankin da su bayar da gudunmawarsu wajen inganta wayar da kan al’umma ta fuskar tsaro da kuma samar da yanayi mai kyau ga kowa da kowa.

Alhaji Zakari Ya’u II, ya kuma jinjinawa daukacin wadanda suka halarci taron buda bakin na shekara shekara, yana mai nuna jin dadinsa bisa hakan, domin wata hanya ce ta sada zumunci a cikin watan Ramadan.

Da yake tsokaci game da mahimmancin taimako kuwa, Sarkin ya gabatar da wani hadisi da ke jaddada taimakon juna a tsakanin al’umma, inda ya bukaci jama’a da su kara jaiki wajen kara karfafa hakkin makwafta da kuma samar da zaman lafiya a cikin al’umma.

Hakazalika Martaba Alhaji Zakari Ya’u II, ya  yi addu’ar samun albarkar watan Ramadan ga dukkan mahalarta taron da iyalansu.

(Na tsakiya) Sakataren Majalisar Masarautar Kauru, Malam Muhammad Sani Suleiman (Dan buran Kauru)

 

A yayin taron, Sakataren Majalisar Masarautar, Malam Muhammad Sani Suleiman wanda shi ke rike da sarautar Dan Buran na Kauru, ya bayyana irin sadaukarwar da Sarkin yakeyi wajen tabbatar da jin dadin al’ummarsa da kuma tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a masarautarsa.

 

Yusuf Zubairu

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai17 hours ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi19 hours ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai3 days ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi3 days ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci3 days ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Fasaha3 days ago

Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ƙaddamar da kashin farko na tsarin karɓar bashin kaya ga ƴan ƙasar. Bayanin hakan na...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Rufe Bankin UBA Kan Kin Biyan Haraji

Hukumar Tara Kudaden Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS) ta raufe rassan bankin UBA kan kin biyan harajin Naira miliyan 14....

Labarai4 days ago

Mutum Biyar Sun Mutu Cikin Kwale-Kwalen ƴan Ci-Rani

Mutum biyar har da yaro sun mutu yayin da suke ƙoƙarin tsallake hanyar ruwa da ta ratsa Ingila da safiyar...

Kasuwanci4 days ago

CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101

Babban Bankin Nigeria CBN ya sake sanar da matakin karya farashin dala daga N1,251 zuwa N1,101. CBN ya bayyana haka...

Ilimi4 days ago

Ƴan Sanda Za Su Yi Bincike Kan Makarantar Leads British

Rundunar ƴan sanda a babban birnin tarayya Abuja ta ce ta aika tawagar jami’anta zuwa makarantar Leads British bayan bidiyon...

Mafi Shahara