Labarai
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
Shugaban hukumar leken asiri ta kasar Isra’ila, Manjo-Janar Aharon Haliva, ya yi murabus saboda harin da ba a taba ganin irinsa ba da kungiyar Hamas ta kai wa kasar.
Manjo- Janar Aharon Haliva, shi ne babban hafsan soji na farko da ya yi murabus bayan caccakar da ya fuskanta kan gagarumin harin na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.
A takardarsa ta barin aiki, Haliva ya ce ya dauki laifin kasa dakile harin da ya sa Hamas ta tsallaka katangar Iyaka da ma duk matakan tsaron Isra’ila har ta kai harin da aka kashe mutane dubu daya da dari daya da talatin da tara, ta kuma yi awon gaba da wasu darruruwa zuwa Gaza, inda ta yi garkuwa da su.
Ana ganin hakan zai bude kofa da manyan jami’an sojin kasar za su dauki laifin harin da ake ganin Hamas ta kada hantar Isra’ila fiye da kowane lokaci.
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai3 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Labarai5 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas