Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin Tarayya dake karamar hukumar Babura.

 

Mataimakin Gwamnan jihar, Injiniya Aminu Usman ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin sabon shugaban gudanarwar jami’ar Oba Ajigbade Gbadegesin Ogunoye Olowo na Owo na uku a ofishinsa dake Dutse babban birnin jihar.

 

Mataimakin Gwamnan wanda ya sami wakilcin Shugaban Ma’aikata na jihar Alhaji Muhammed Dagacheri, yace Gwamna Umar Namadi ya bada umarnin gina gidaje da kuma samar da kayayyakin koyo da koyarwa domin baiwa malaman jami’ar kwarin gwiwar gudanar da ayyukan su.

 

Kazalika, ya bada tabbacin gwamnatin jihar na ci gaba da tallafawa jami’ar domin amfanin ‘yan jiha da ma kasa baki daya.

 

A jawabin sa, sabon shugaban gudanarwar jami’ar, basarake Oba Ajigbade ya yabawa gwamnatin jihar Jigawan bisa tallafawa jami’ar a koda yaushe.

 

A don haka, ya bada tabbacin ciyar da Jami’ar gaba a matsayinsa na shugaban gudanarwarta na farko, tare da neman hadin kan gwamnatin da ma al’ummar jihar domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Tun farko a jawabin sa, shugaban jami’ar Farfesa Sabo Birnin Kudu yace sun zo ofishin mataimakin Gwamnan ne domin gabatar da sabon shugaban gudanarwar jami’ar da kuma godewa gwamnatin jihar bisa tallafin da take bai wa jami’ar.

 

Yana mai cewar jami’ar ta na da yawan dalibai dubu daya da ma’aikata 180 da kuma Kwasa-kwasai guda goma sha takwas da take gudanarwa.

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai2 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai2 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai2 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi2 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai3 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai3 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai4 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai4 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai4 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara