Ilimi
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin Tarayya dake karamar hukumar Babura.
Mataimakin Gwamnan jihar, Injiniya Aminu Usman ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin sabon shugaban gudanarwar jami’ar Oba Ajigbade Gbadegesin Ogunoye Olowo na Owo na uku a ofishinsa dake Dutse babban birnin jihar.
Mataimakin Gwamnan wanda ya sami wakilcin Shugaban Ma’aikata na jihar Alhaji Muhammed Dagacheri, yace Gwamna Umar Namadi ya bada umarnin gina gidaje da kuma samar da kayayyakin koyo da koyarwa domin baiwa malaman jami’ar kwarin gwiwar gudanar da ayyukan su.
Kazalika, ya bada tabbacin gwamnatin jihar na ci gaba da tallafawa jami’ar domin amfanin ‘yan jiha da ma kasa baki daya.
A jawabin sa, sabon shugaban gudanarwar jami’ar, basarake Oba Ajigbade ya yabawa gwamnatin jihar Jigawan bisa tallafawa jami’ar a koda yaushe.
A don haka, ya bada tabbacin ciyar da Jami’ar gaba a matsayinsa na shugaban gudanarwarta na farko, tare da neman hadin kan gwamnatin da ma al’ummar jihar domin kwalliya ta biya kudin sabulu.
Tun farko a jawabin sa, shugaban jami’ar Farfesa Sabo Birnin Kudu yace sun zo ofishin mataimakin Gwamnan ne domin gabatar da sabon shugaban gudanarwar jami’ar da kuma godewa gwamnatin jihar bisa tallafin da take bai wa jami’ar.
Yana mai cewar jami’ar ta na da yawan dalibai dubu daya da ma’aikata 180 da kuma Kwasa-kwasai guda goma sha takwas da take gudanarwa.
Usman Mohammed Zaria
-
Labarai3 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha4 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai4 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai2 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai4 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar