Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Zai Biya Tallafin Naira Miliyan 1 Ga Kowani Mahajjaci

Published

on

Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya amince da biyan tallafin Naira miliyan daya ga kowane mahajjaci daga jihar don yin aikin Hajjin bana a karkashin hukumar jin dadin alhazai ta jihar.

 

Shugaban hukumar jin dadin alhazai ta jihar jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga gidan rediyon Najeriya a Dutse babban birnin jihar.

 

A cewarsa, Gwamnan ya dauki matakin ne dangane da karin kudin Hajji da Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta yi a baya-bayan nan wanda aka alakanta shi da rashin daidaiton farashin canji.

 

Akwai mutanen da suka rigaya suka biya gaba daya, amma kwatsam sai aka samu karin kudin aikin Hajji, karin kudin aikin Hajji babban kalubale ne ga dimbin maniyyata.” Inji shi.

Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Ahmad Umar Labo

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bukaci dukkan maniyyatan jihar da su tabbatar sun biya sauran kudaden da suka rage wato  naira dubu dari tara da goma sha takwas ga hukumar.

 

Shugaban hukumar ya yi nuni da cewa wadanda za su ci gajiyar tallafin aikin Hajjin su ne wadanda dama sun biya kudin aikin Hajjin ga hukumar.

 

Idan dai za a iya tunawa, NAHCON ta sanar da karin kudin aikin Hajji da Naira miliyan daya da dubudaritaradagomashatakwas, wanda ya sa adadin kudin aikin Hajji ya kai naira miliyan shuda da dubu dari shida da goma sha bakwai.

 

 

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai16 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai18 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai19 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi19 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara