Labarai
Gwamna Namadi Zai Biya Tallafin Naira Miliyan 1 Ga Kowani Mahajjaci
Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya amince da biyan tallafin Naira miliyan daya ga kowane mahajjaci daga jihar don yin aikin Hajjin bana a karkashin hukumar jin dadin alhazai ta jihar.
Shugaban hukumar jin dadin alhazai ta jihar jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga gidan rediyon Najeriya a Dutse babban birnin jihar.
A cewarsa, Gwamnan ya dauki matakin ne dangane da karin kudin Hajji da Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta yi a baya-bayan nan wanda aka alakanta shi da rashin daidaiton farashin canji.
“Akwai mutanen da suka rigaya suka biya gaba daya, amma kwatsam sai aka samu karin kudin aikin Hajji, karin kudin aikin Hajji babban kalubale ne ga dimbin maniyyata.” Inji shi.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bukaci dukkan maniyyatan jihar da su tabbatar sun biya sauran kudaden da suka rage wato naira dubu dari tara da goma sha takwas ga hukumar.
Shugaban hukumar ya yi nuni da cewa wadanda za su ci gajiyar tallafin aikin Hajjin su ne wadanda dama sun biya kudin aikin Hajjin ga hukumar.
Idan dai za a iya tunawa, NAHCON ta sanar da karin kudin aikin Hajji da Naira miliyan daya da dubudaritaradagomashatakwas, wanda ya sa adadin kudin aikin Hajji ya kai naira miliyan shuda da dubu dari shida da goma sha bakwai.
Usman Muhammad Zaria
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai6 days ago
An Kashe Makiyaya 2 Da Shanu 150 A Sabon Hari A Filato