Kasuwanci
An Fasa Rumbun Abincin Gwamnati A Jihar Kebbi
Wasu mutane sun fasa rumbun abincin gwamnati a Jihar Kebbi da ke Unguwar Bayan Kara a Birnin Kebbi a ranar Lahadi.
Mutanen da suka fasa rumbun sun yi galaba ne a kan jami’an tsaron da ke tsare da rumbun na gwamnati.
An bayyana cewa bayan Rumbun Gwamnati da aka fasa, mutanen sun wawushe kayan abincin da ke makare a wata mota da ta lalace a kan hanya.
Shugaban ’yan kasuwar Bayan Kara dake Birnin Kebbi Muhammadu Gwadangwaji ya ce, ba Rumbun Gwamnati kadai mutane suka fasa ba.
A cewarsa, an fasa wasu shagunan ’yan kasuwa an kuma cinna wa wasu wuta, duk da irin ƙoƙarin da jami’an tsaro suka yi.
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris; Ahmed Idris, ya bayyana lamarin a matsayin “abin takaici”.
Ya bayyana cewa: “Tun da farko an samu wasu ɓata-gari sun kai hari kan kayan abinci da Dangote ya aiko jiharmu domin rabawa jama’a sannan suka garzaya ma’ajiyar gwamnati inda nan ma suka kwashe wasu kayan abincin.
“Irin wannan lamari bai taba faruwa a Kebbi ba. Kayayyakin abincin da suka wawashe na daga cikin kayan abincin da gwamnatin jihar ta siya domin raba wa al’umma“.
Ya ce, gwamnati ta ɗauki matakin kare ma’ajiyar ta domin hana afkuwar irin haka anan gaba.
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Labarai13 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert
-
Labarai19 mins ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas