Connect with us

Ilimi

Kebbi Ta Zuba Biliyoyin Naira Don Saukaka Rayuwar ‘Yan Kasa – Inji Kwamishinan Yada Labarai

Published

on

 

Gwamnatin Gwamna Nasir Idris a jihar Kebbi, yace sun kashe biliyoyin kudade daga ranar 29 ga watan Mayu, 2023 don rage dimbin radadin da al’ummarta ke fama da su, tare da juya dukiyoyin jihar fiye da yadda ya gada.

 

Kwamishinan Yada Labarai da Al’adu Alhaji Yakubu Ahmed Birnin Kebbi, wanda ya bayyana haka a taron manema labarai da ma’aikatar yada labarai da al’adu ta shirya, ya jaddada cewa, Gwamnan ya yi nasarar kawo sauyi a Jihar Kebbi ta bangarori daban-daban na rayuwar dan Adam.

 

“Misali, matsalar da al’umma ke fama da su a halin da ake ciki na tabarbarewar tattalin arziki, Gwamnan ya sayi hatsi iri-iri na sama da Naira biliyan 12, ya raba wa ‘yan jihar kyauta. Ya kara da cewa, tallafin ya kai ga dukkan nau’o’in jama’ar jihar.

 

Kwamishinan ya ce, dole ne a yaba wa gwamnatin jihar Kebbi kan yadda ta raba kayan agaji ga kowane fanni na rayuwa, ba tare da la’akari da wata alaka ta siyasa ko addini ba.

 

Dangane da batun samar da abinci, Kwamishinan ya bayyana cewa, kokari da matakan da gwamnatin Nasiru Idris ta danka sun yi nisa wajen tabbatar da samar da abinci da kuma tabbatar da cewa al’ummar jihar ba su taba fuskantar yunwa ba.

 

A cewar Kwamishinan, gwamnatin ta kashe makudan kudade wajen siyan kayayyakin amfanin gona iri-iri da kayan aiki tare da raba wa manoman a fadin jihar kyauta baya ga feshin tsuntsayen da ake yi.

 

Ya kuma yi kira ga ‘yan adawa da masu fafutuka da su daina kamfen din zagon kasa ga gwamnatin Nasiru Idris domin baiwa gwamnan damar mayar da hankali kan ayyukan da jama’a suka zabi shi ya gudanar.

 

Abdullahi Tukur/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai2 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai5 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara