Connect with us

Labarai

Akalla Mutane 10 Sun Mutu A Turmutsitsin Karbar Kayan Sallah A Sakkwato

Published

on

A kalla mutane goma ne suka mutu yayin da wasu da ba a tantance adadinsu ba suka samu raunuka sakamakon turmutsitsin da ya faru a Sokoto.

 

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na babbar jam’iyyar adawa ta PDP a jihar, Hassan Sahabi Sanyinna ya fitar, ya ce turmutsitsin ya faru ne sakamakon rashin tsari na rabon kayan abinci da suturar Sallah ga jama’a a unguwar Gawon Nama wanda gida ne na Jagoran jam’iyyar APC mai mulki a jihar, Sanata Alu Magatakardan Wamako.

 

A cewar sanarwar, wata jami’ar hukumar tsaron farin kaya ta kasa na daga cikin mutane goma da suka mutu a wannan mummunan lamari.

 

Sanarwar ta mika sakon jaje ga iyalan wadanda suka rasu yayin da suke addu’ar samun lafiya, ga wadanda suka samu raunuka a wurin da lamarin ya faru.

 

Sannan ta yi kira ga jami’an tsaro su kaddamar da cikakken bincike kan lamarin, da nufin hana sake faruwar haka a nan gaba.

 

Sanarwar ta kuma bukaci a biya diyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wasu da suka jikkata a lamarin.

 

Hakazalika, sanarwar da wasu jama’a ba su tabbatar ba, sun nuna cewa sama da mutane goma sha biyar ne suka rasa rayukansu a turmutsutsun.

 

Kokarin da gidan rediyon Najeriya ya yi na tabbatar da faruwar lamarin daga rundunar ‘yan sandan Najeriya da jami’an tsaron farin kaya bai yi nasara ba.

 

NASIR MALALI/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai7 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai8 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai21 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara