Connect with us

Labarai

Akalla Mutane 10 Sun Mutu A Turmutsitsin Karbar Kayan Sallah A Sakkwato

Published

on

A kalla mutane goma ne suka mutu yayin da wasu da ba a tantance adadinsu ba suka samu raunuka sakamakon turmutsitsin da ya faru a Sokoto.

 

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na babbar jam’iyyar adawa ta PDP a jihar, Hassan Sahabi Sanyinna ya fitar, ya ce turmutsitsin ya faru ne sakamakon rashin tsari na rabon kayan abinci da suturar Sallah ga jama’a a unguwar Gawon Nama wanda gida ne na Jagoran jam’iyyar APC mai mulki a jihar, Sanata Alu Magatakardan Wamako.

 

A cewar sanarwar, wata jami’ar hukumar tsaron farin kaya ta kasa na daga cikin mutane goma da suka mutu a wannan mummunan lamari.

 

Sanarwar ta mika sakon jaje ga iyalan wadanda suka rasu yayin da suke addu’ar samun lafiya, ga wadanda suka samu raunuka a wurin da lamarin ya faru.

 

Sannan ta yi kira ga jami’an tsaro su kaddamar da cikakken bincike kan lamarin, da nufin hana sake faruwar haka a nan gaba.

 

Sanarwar ta kuma bukaci a biya diyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wasu da suka jikkata a lamarin.

 

Hakazalika, sanarwar da wasu jama’a ba su tabbatar ba, sun nuna cewa sama da mutane goma sha biyar ne suka rasa rayukansu a turmutsutsun.

 

Kokarin da gidan rediyon Najeriya ya yi na tabbatar da faruwar lamarin daga rundunar ‘yan sandan Najeriya da jami’an tsaron farin kaya bai yi nasara ba.

 

NASIR MALALI/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai1 day ago

Muna Tare Da Gwamnatin Bola Tinubu – Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa

Gamayyar Kungiyoyin MatasanJihohin Arewa Na 19 Sun Ce ko kadan ba sa goyon bayan Zanga-zangar, domin Barazana ce Ga Tsaron...

Labarai1 day ago

‘Yansanda Sun Sake Kama Masu Zanga-Zanga 70 A Uganda

An kama masu zanga-zanga da dama wadanda suka halarci wani haramtaccen gangami da aka gudanar a Kampala babban birnin Uganda,...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Wa Masu Shirin Zanga-Zanga Gargadi

Rundunar Tsaron Najeriya ta gargadi masu shirin zanga-zangar yaki da tsadar rayuwa a Najeriya ta ce sojoji ba za su...

Labarai2 days ago

Olympics: ‘Yan Matan Najeriya Za Su Kara Da Na Brazil

A yau Alhamis ne ƙungiyar Super Falcons ta ‘yan ƙwallon matan Najeriya za su kara da takwarorinsu na Brazil a...

Labarai2 days ago

Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Kungiyar Sanatocin Arewa ta yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa rattaba hannu kan kudirin hukumar raya yankin Arewa maso...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Bukatar Gudanar Da Zaben Kananan Hukumomi

Majalisar zartaswar jihar Jigawa ta amince da bukatar hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar, na gudanar da zaben kananan...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Shugaban kasa Bola Tinubu ya rattaba hannu  kan kudirin doka don hanzarta samar da ci gaba a shiyyoyin kasar nan....

Labarai3 days ago

Za’a Fara Wasannin Olympics A Faransa

Yayin da ake dab da fara gasar wasannin motsa jiki ta bazara wato Olympic, ta shekarar 2024 a birnin Paris...

Labarai3 days ago

‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda

Ƴanjarida a ƙasar Kenya za su gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar domin nuna adawa da zargin cin zalin da...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Rabon Tallafi Ga Kananan ‘Yan Kasuwa A Jigawa

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bukaci matasa da su guji yin zanga-zanga a kasa. Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ne ya...

Mafi Shahara