Labarai
Akalla Mutane 10 Sun Mutu A Turmutsitsin Karbar Kayan Sallah A Sakkwato
![](https://radionigeriakaduna.gov.ng/hausa/wp-content/uploads/2024/04/unnamed.jpg)
A kalla mutane goma ne suka mutu yayin da wasu da ba a tantance adadinsu ba suka samu raunuka sakamakon turmutsitsin da ya faru a Sokoto.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na babbar jam’iyyar adawa ta PDP a jihar, Hassan Sahabi Sanyinna ya fitar, ya ce turmutsitsin ya faru ne sakamakon rashin tsari na rabon kayan abinci da suturar Sallah ga jama’a a unguwar Gawon Nama wanda gida ne na Jagoran jam’iyyar APC mai mulki a jihar, Sanata Alu Magatakardan Wamako.
A cewar sanarwar, wata jami’ar hukumar tsaron farin kaya ta kasa na daga cikin mutane goma da suka mutu a wannan mummunan lamari.
Sanarwar ta mika sakon jaje ga iyalan wadanda suka rasu yayin da suke addu’ar samun lafiya, ga wadanda suka samu raunuka a wurin da lamarin ya faru.
Sannan ta yi kira ga jami’an tsaro su kaddamar da cikakken bincike kan lamarin, da nufin hana sake faruwar haka a nan gaba.
Sanarwar ta kuma bukaci a biya diyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wasu da suka jikkata a lamarin.
Hakazalika, sanarwar da wasu jama’a ba su tabbatar ba, sun nuna cewa sama da mutane goma sha biyar ne suka rasa rayukansu a turmutsutsun.
Kokarin da gidan rediyon Najeriya ya yi na tabbatar da faruwar lamarin daga rundunar ‘yan sandan Najeriya da jami’an tsaron farin kaya bai yi nasara ba.
NASIR MALALI/Wababe
-
Labarai6 days ago
Al’ummar Kauru Na Cikin Zullumi Bayan Lalacewar Gadar Da Ta Hadasu Da sauran Al’ummomin Jihar Kaduna
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Harkar Noma A Yobe
-
Labarai2 days ago
Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
-
Kasuwanci4 days ago
An Shawarci Matasan Jihar Niger Su Guji Shiga Zanga-Zangar Babu Gaira Babu Dalili
-
Labarai3 days ago
Zanga Zanga: Gwamnati Ta Baiwa Matasa Tabbacin Daukan Bukatun Su Da Mahimmanci
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Kano Za Ta Samar Da Kananan Jiragen Ruwa A Kananan Hukumomi 3
-
Labarai3 days ago
‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda
-
Labarai4 days ago
Taurarin Finafinan Hausa Na Alhinin Rasuwar Sulaiman Alaka