Labarai
Akalla Mutane 10 Sun Mutu A Turmutsitsin Karbar Kayan Sallah A Sakkwato
A kalla mutane goma ne suka mutu yayin da wasu da ba a tantance adadinsu ba suka samu raunuka sakamakon turmutsitsin da ya faru a Sokoto.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na babbar jam’iyyar adawa ta PDP a jihar, Hassan Sahabi Sanyinna ya fitar, ya ce turmutsitsin ya faru ne sakamakon rashin tsari na rabon kayan abinci da suturar Sallah ga jama’a a unguwar Gawon Nama wanda gida ne na Jagoran jam’iyyar APC mai mulki a jihar, Sanata Alu Magatakardan Wamako.
A cewar sanarwar, wata jami’ar hukumar tsaron farin kaya ta kasa na daga cikin mutane goma da suka mutu a wannan mummunan lamari.
Sanarwar ta mika sakon jaje ga iyalan wadanda suka rasu yayin da suke addu’ar samun lafiya, ga wadanda suka samu raunuka a wurin da lamarin ya faru.
Sannan ta yi kira ga jami’an tsaro su kaddamar da cikakken bincike kan lamarin, da nufin hana sake faruwar haka a nan gaba.
Sanarwar ta kuma bukaci a biya diyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wasu da suka jikkata a lamarin.
Hakazalika, sanarwar da wasu jama’a ba su tabbatar ba, sun nuna cewa sama da mutane goma sha biyar ne suka rasa rayukansu a turmutsutsun.
Kokarin da gidan rediyon Najeriya ya yi na tabbatar da faruwar lamarin daga rundunar ‘yan sandan Najeriya da jami’an tsaron farin kaya bai yi nasara ba.
NASIR MALALI/Wababe
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai21 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Labarai7 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert