Connect with us

Labarai

Kotu ta nemi yansanda su biya matan da suka tilasta wa tube hijabi dala miliyan 17

Published

on

Rundunar ‘yan sandan birnin New York za ta biya dala miliyan 17.5, a wani shari’ar da wasu mata Musulmi suka jagoranta, waɗanda aka tilasta musu cire hijabi yayin da aka ɗauki hotonsu.

Shari’ar ta 2018 ta bayar da hujjar cewa Jamilla Clark da Arwa Aziz sun fuskanci cin zarafi na ‘yancin yin addini da kuma ta rayuwa.

Lauyoyi sun ce sama da mutum 3,600 ne suka cancanci a biya su karkashin yarjejeniyar.

Ƴan sanda sun canza tsari shekaru huɗu da suka gabata don ba da izinin sanya hijabi.

Birnin ya ce lamarin ya haifar da sauyi mai kyau.

Dole ne alkali na tarayya da ke sa ido kan shari’ar ya amince da yarjejeniyar biyan diyyar.

Kamar yadda bayanan kotun suka nuna, Ms Clark ta yi kuka tare da rokon a bar ta saka hijabinta yayin da ‘yan sanda suka ɗauki hotonta.

“Lokacin da suka tilasta min cire hijabi na, sai na ji kamar tsirara nake, bani da tabbacin ko kalmomi za su iya kwatanta yadda nake ji da kuma cin zarafina da aka yi,” in ji Ms Clark a wata sanarwa a ranar Juma’a.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai5 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai2 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai5 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara