Labarai
Kotu ta nemi yansanda su biya matan da suka tilasta wa tube hijabi dala miliyan 17
![](https://radionigeriakaduna.gov.ng/hausa/wp-content/uploads/2024/04/7f6725b6-9cf1-498a-ac4c-c6acecbecd12.jpg)
Rundunar ‘yan sandan birnin New York za ta biya dala miliyan 17.5, a wani shari’ar da wasu mata Musulmi suka jagoranta, waɗanda aka tilasta musu cire hijabi yayin da aka ɗauki hotonsu.
Shari’ar ta 2018 ta bayar da hujjar cewa Jamilla Clark da Arwa Aziz sun fuskanci cin zarafi na ‘yancin yin addini da kuma ta rayuwa.
Lauyoyi sun ce sama da mutum 3,600 ne suka cancanci a biya su karkashin yarjejeniyar.
Ƴan sanda sun canza tsari shekaru huɗu da suka gabata don ba da izinin sanya hijabi.
Birnin ya ce lamarin ya haifar da sauyi mai kyau.
Dole ne alkali na tarayya da ke sa ido kan shari’ar ya amince da yarjejeniyar biyan diyyar.
Kamar yadda bayanan kotun suka nuna, Ms Clark ta yi kuka tare da rokon a bar ta saka hijabinta yayin da ‘yan sanda suka ɗauki hotonta.
“Lokacin da suka tilasta min cire hijabi na, sai na ji kamar tsirara nake, bani da tabbacin ko kalmomi za su iya kwatanta yadda nake ji da kuma cin zarafina da aka yi,” in ji Ms Clark a wata sanarwa a ranar Juma’a.
-
Labarai7 days ago
Al’ummar Kauru Na Cikin Zullumi Bayan Lalacewar Gadar Da Ta Hadasu Da sauran Al’ummomin Jihar Kaduna
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Harkar Noma A Yobe
-
Labarai2 days ago
Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
-
Kasuwanci4 days ago
An Shawarci Matasan Jihar Niger Su Guji Shiga Zanga-Zangar Babu Gaira Babu Dalili
-
Labarai4 days ago
Zanga Zanga: Gwamnati Ta Baiwa Matasa Tabbacin Daukan Bukatun Su Da Mahimmanci
-
Labarai3 days ago
‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Za Ta Samar Da Kananan Jiragen Ruwa A Kananan Hukumomi 3
-
Labarai4 days ago
Taurarin Finafinan Hausa Na Alhinin Rasuwar Sulaiman Alaka