Ilimi
Maniyyata 51,447 Ne Za Su Sauke Farali A Aikin Hajjin Bana – NAHCON
![](https://radionigeriakaduna.gov.ng/hausa/wp-content/uploads/2024/04/546472ce-2976-4886-bdba-4b778653ccfd.jpg)
Hukumar Alhazai ta Najeriya, ta ce aƙalla maniyyatan Najeriya 51,447 ne za su sauke farali a aikin Hajjin bana a ƙasar Saudiyya.
Shugaban hukumar, Malam Jalal Arabi, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar ranar Juma’a a Abuja.
Arabi ya ce hukumar na tsare-tsare wajen ganin ta gudanar da aikin Hajji cikin nasara, ko da kuwa za a fuskanci kalubale.
Ya nanata cewa Msulman Najeriya za su yi aikin Hajjin 2024 a adadin da babu wanda ya taɓa tunani.
“Shirye-shiryen Hajjin bana na ɗaya daga cikin mafi wahala da aka taɓa gani,” in ji shi.
Ya ce a baya, an samu lokaci mai yawa na yin shirin da ya kamata, amma a wannan karon, Saudiyya ba ta ba su isasshen lokaci ba.
Malam Arabi ya ce gwamnatin tarayya ta shiga taimaka ta hanyoyi da dama, musamman ma ɓullo da wasu tsare-tsare na tallafa wa hukumar domin tabbatar da cewa al’amura su tafi yadda ya dace.
Ma’aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya ta ware wa Najeriya kujeru 95,000 domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2024.
-
Labarai6 days ago
Al’ummar Kauru Na Cikin Zullumi Bayan Lalacewar Gadar Da Ta Hadasu Da sauran Al’ummomin Jihar Kaduna
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Harkar Noma A Yobe
-
Labarai2 days ago
Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
-
Kasuwanci4 days ago
An Shawarci Matasan Jihar Niger Su Guji Shiga Zanga-Zangar Babu Gaira Babu Dalili
-
Labarai3 days ago
Zanga Zanga: Gwamnati Ta Baiwa Matasa Tabbacin Daukan Bukatun Su Da Mahimmanci
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Kano Za Ta Samar Da Kananan Jiragen Ruwa A Kananan Hukumomi 3
-
Labarai3 days ago
‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda
-
Labarai4 days ago
Taurarin Finafinan Hausa Na Alhinin Rasuwar Sulaiman Alaka