Connect with us

Ilimi

Maniyyata 51,447 Ne Za Su Sauke Farali A Aikin Hajjin Bana – NAHCON

Published

on

Hukumar Alhazai ta Najeriya, ta ce aƙalla maniyyatan Najeriya 51,447 ne za su sauke farali a aikin Hajjin bana a ƙasar Saudiyya.

Shugaban hukumar, Malam Jalal Arabi, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar ranar Juma’a a Abuja.

Arabi ya ce hukumar na tsare-tsare wajen ganin ta gudanar da aikin Hajji cikin nasara, ko da kuwa za a fuskanci kalubale.

Ya nanata cewa Msulman Najeriya za su yi aikin Hajjin 2024 a adadin da babu wanda ya taɓa tunani.

“Shirye-shiryen Hajjin bana na ɗaya daga cikin mafi wahala da aka taɓa gani,” in ji shi.

Ya ce a baya, an samu lokaci mai yawa na yin shirin da ya kamata, amma a wannan karon, Saudiyya ba ta ba su isasshen lokaci ba.

Malam Arabi ya ce gwamnatin tarayya ta shiga taimaka ta hanyoyi da dama, musamman ma ɓullo da wasu tsare-tsare na tallafa wa hukumar domin tabbatar da cewa al’amura su tafi yadda ya dace.

Ma’aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya ta ware wa Najeriya kujeru 95,000 domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2024.

Labarai

Labarai1 day ago

Muna Tare Da Gwamnatin Bola Tinubu – Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa

Gamayyar Kungiyoyin MatasanJihohin Arewa Na 19 Sun Ce ko kadan ba sa goyon bayan Zanga-zangar, domin Barazana ce Ga Tsaron...

Labarai1 day ago

‘Yansanda Sun Sake Kama Masu Zanga-Zanga 70 A Uganda

An kama masu zanga-zanga da dama wadanda suka halarci wani haramtaccen gangami da aka gudanar a Kampala babban birnin Uganda,...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Wa Masu Shirin Zanga-Zanga Gargadi

Rundunar Tsaron Najeriya ta gargadi masu shirin zanga-zangar yaki da tsadar rayuwa a Najeriya ta ce sojoji ba za su...

Labarai2 days ago

Olympics: ‘Yan Matan Najeriya Za Su Kara Da Na Brazil

A yau Alhamis ne ƙungiyar Super Falcons ta ‘yan ƙwallon matan Najeriya za su kara da takwarorinsu na Brazil a...

Labarai2 days ago

Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Kungiyar Sanatocin Arewa ta yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa rattaba hannu kan kudirin hukumar raya yankin Arewa maso...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Bukatar Gudanar Da Zaben Kananan Hukumomi

Majalisar zartaswar jihar Jigawa ta amince da bukatar hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar, na gudanar da zaben kananan...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Shugaban kasa Bola Tinubu ya rattaba hannu  kan kudirin doka don hanzarta samar da ci gaba a shiyyoyin kasar nan....

Labarai3 days ago

Za’a Fara Wasannin Olympics A Faransa

Yayin da ake dab da fara gasar wasannin motsa jiki ta bazara wato Olympic, ta shekarar 2024 a birnin Paris...

Labarai3 days ago

‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda

Ƴanjarida a ƙasar Kenya za su gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar domin nuna adawa da zargin cin zalin da...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Rabon Tallafi Ga Kananan ‘Yan Kasuwa A Jigawa

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bukaci matasa da su guji yin zanga-zanga a kasa. Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ne ya...

Mafi Shahara