Connect with us

Ilimi

Hukumar Zakka da Waƙafi ta Jihar Zamfara…

Published

on

Hukumar Zakka da Waƙafi ta Jihar Zamfara

Fata Ga Marasa Galihu Da Kawo Canji A Rayuwar Jama’a

Daga Abdullahi Musa

A ‘yan makonnin da suka gabata ne Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin Sheikh Umar Ahmad Kanoma, ta bullo da wasu sabbin hanyoyi da tsare-tsaren taimaka wa wajen canja rayuwar al’umma da kyautata jin dadin da kuma zamantakewarsu.

Hukumar ta ƙarfafa hanyoyin da aka san ta su na jajircewa wajen yi wa al’umma hidima cikin tausayi da adalci, Hukumar ta samu gagarumin ci gaba a ayyukanta na rage radadin talauci da ƙarfafa wa marasa galihu a lokacin Azumin watan Ramadan da ya gabata.

Bisa kulawar sakataren zartaswa, Habib Balarabe Muhammad, Hukumar ta samu gagarumar nasara wajen tallafa wa mabuƙata da marasa galihu.

Hukumar ta Kai ɗaukin gaggawa ga mata masu fama da matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da haifar masu da fata a zukatansu, ta hanyar shirya masu tarukan fadakarwa da nufin kyautata rayuwarsu.

Baya ga samar wa mata da matasa marasa galihu hanyoyin dogaro da kai, Hukumar ta tallafa masu da mahimman kayayyakin koyon sana’a da haɓaka ƙwarewa a tsakaninsu. Wannan tsarin jin kai yana nuna sadaukarwar Hukumar don jindadin marasa galihu.

A cikin watan Ramadan, Hukumar ta kara kaimi, inda ta tallafa wa mutane sama da 40,000 a fadin jihar Zamfara da kayan abinci da taimakon kuɗi.

Bugu da ƙari, Hukumar ta samar da gaɓoɓin roba kyauta ga mutanen da rasa gaɓoɓinsu sakamako hattsura ko ayyukan ‘yan ta’adda da taimaka wa mata masu matsalar cutar yoyon fitsari (VVF). Hakan ya jaddada himmar Hukumar wajen samun damar kiwon lafiya da nufin inganta rayuwar marasa galihu.

Ta hanyar haɗin gwiwa da ƙungiyoyi jin kai kamar; Bright Futures Serious da Organised Crime Prevention Project (SOC), Hukumar ta samar da tsare-tsare don rigakafi da kuma tsarin tallafi, tabbatar da samari masu aikata laifuka sun sami jagoranci na gari a rayuwarsu da nufin ƙarfafa su don kawar da aikata miyagun laifuka a tsakanin al’umma a jihar.

Bayan Eid al-Fitr, Hukumar ta kasance mai himma, tare da yin alƙawarin shigar ɗaruruwan mutane a cikin shirye-shiryen gina rayuwarsu da dabarun haɓaka fasaha. Wannan tsarin sa ido yana nuna sadaukarwarsu ga ƙarfafawa ta dogon lokaci da nufin samar da mafita mai dorewa ga al’umma.

Nasarorin da Hukumar ke samu sun nuna muhimmancin samar da kyakkyawan tsari daa irin tasirin da yake da shi. Tun daga yunkurin agajin gaggawa zuwa shirye-shiryen karfafawa na dogon lokaci, kowane aiki yana kunshe da ka’idojin hadin gwiwa da jin kai da ke cikin Zakka.

Hukumar ta yi alƙawarin kiyaye ƙa’idodin aiki, haɓaka haɗin gwiwa, da bullo da sabbin hanyoyi don magance talauci da kuma fuskantar ƙalubalen tattalin arziki yadda ya kamata.

Tare da jajircewa wajen yi wa al’umma hidima bisa tsarin addinin Musulunci, Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar Zamfara ta tsaya tsayin daka a matsayin wata fitilar da ke haskaka rayuwar marasa galihu da kuma samar masu da fata a rayuwa.

Fassara/Wababe/ Caliphate Times

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai11 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara