Labarai
Waɗanda suka dakatar da Ganduje ba ƴan APC ba ne – Abdullahi Abbas
Jam’iyyar APC a jihar Kano ta ce za ta ɗauki mataki kan ɓangaren da ya sanar da dakatar da tsohon gwamnan jihar kuma shugaban jam’iyyar APC ta ƙasa na riƙo, Abdullahi Umar Ganduje.
A ranar Litinin ne wani reshen mazaɓar Ganduje da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano ya sanar da dakatar da shugaban jam’iyyar ta kasa, daga bisani kuma shugaban jam’iyyar APC din a matakin ƙaramar hukumar Dawakin Tofa ya yi watsi da matakin.
Shugaban jam’iyyar APC a jihar, Abdullahi Abbas ya yi zargin cewa waɗanda suka dakatar da Ganduje makusanta ne ga wasu masu riƙe da muƙamai a gwamnatin jihar da NNPP ke mulki.
Ya shaida cewa sun duba jerin sunayen ƴan jam’iyyar na mazaɓar Ganduje, “mutum 27 ne kowace mazaɓa, mun duba a cikin su gaba ɗaya babu ko ɗaya da yake a cikin shugabanni.”
A cewarsa, jami’in da aka ce ya sanar da dakatar da Gandujen, Haladu Gwanjo, ya ce zai je kotu ya nemi haƙƙinsa saboda an zalunce shi.
Abdullahi Abbas ya bayyana cewa “wannan ba abin da ya haɗa shi da jam’iyyarmu, wannan tsari ne na gwamnatin jihar Kano da jam’iyyarsu ta kayan gwari suka shirya, ina tunanin wannan [ita ce] hanyar da za su ci mutuncin dakta Ganduje.”
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai22 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Labarai9 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Kasuwanci4 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi4 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert