Labaran Ketare
Isra’ila ta ƙaddamar da hari kan asibitin al-Shifa a Gaza
Sojojin Isra’ila sun sanar da ƙaddamar da hari kan asibitin al-Shifa da ke Gaza.
Mai magana da yawun sojin Isra’ilar, Rear Admiral Daniel Hagari, ya ce sojoji sun gano matattarar Hamas da sake shiri ta amfani da asibitin domin kai musu hari.
Hagari ya ce “muna kira ga ‘yan ta’addar Hamas da ke ɓuya a asibitoci, su mika wuya ba tare da ɓata lokaci ba, asibitoci ba wurin aikata ta’addanci ba ne”.
Wani bidiyo da aka aike wa BBC ya nuna ɗaruruwan farar hula na ficewa daga asibitin, cikin tsananin duhu suna amfani da hasken wayar salula domin haska hanya.
Wata sanarwa daga ma’aikatar lafiyar Hamas ta kira harin a matsayin take dokar jin ƙai ta ƙasa da ƙasa”.
Ɗaruruwan Falasɗinawa da suka ɗaiɗaita ne ke samun mafaka a asibitin da sojojin Isra’ila suka kai wa samame a farkon soma yaƙin.
Al-Shifa shi ne babban asibitin Gaza kafin yaƙin amma ayyukansa sun fuskanci cikas bayan shafe watanni ana gumurzu.
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai7 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Labarai6 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha1 day ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci1 day ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Fasaha1 day ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet