Connect with us

Labaran Ketare

Isra’ila ta ƙaddamar da hari kan asibitin al-Shifa a Gaza

Published

on

Sojojin Isra’ila sun sanar da ƙaddamar da hari kan asibitin al-Shifa da ke Gaza.

Mai magana da yawun sojin Isra’ilar, Rear Admiral Daniel Hagari, ya ce sojoji sun gano matattarar Hamas da sake shiri ta amfani da asibitin domin kai musu hari.

Hagari ya ce “muna kira ga ‘yan ta’addar Hamas da ke ɓuya a asibitoci, su mika wuya ba tare da ɓata lokaci ba, asibitoci ba wurin aikata ta’addanci ba ne”.

Wani bidiyo da aka aike wa BBC ya nuna ɗaruruwan farar hula na ficewa daga asibitin, cikin tsananin duhu suna amfani da hasken wayar salula domin haska hanya.

Wata sanarwa daga ma’aikatar lafiyar Hamas ta kira harin a matsayin take dokar jin ƙai ta ƙasa da ƙasa”.

Ɗaruruwan Falasɗinawa da suka ɗaiɗaita ne ke samun mafaka a asibitin da sojojin Isra’ila suka kai wa samame a farkon soma yaƙin.

Al-Shifa shi ne babban asibitin Gaza kafin yaƙin amma ayyukansa sun fuskanci cikas bayan shafe watanni ana gumurzu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai6 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai6 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci1 day ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha1 day ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha1 day ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai1 day ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara