Labarai
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido daga Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON domin tantance ayyukan hukumar.
A jawabin shugabar tawagar kuma babbar jami’ar hukumar ta NAHCON a jihar Jigawa Hajiya Rabi’atu Dahiru Nyako, ta bayyana cewa manufar ziyarar ita ce tantance kayayyakin aikin hukumar tare da duba yaddatake gudanarda shirye-shiryen aikin Hajjin bana.
“Tawagar za ta tantance kayan aiki, da shirye-shiryen jigilar maniyyatan jihar, da takardun tafiya kasa mai tsarki, da fasfo fasfo da sauransu”.
Babbar Jami’iar ta bayyana gamsuwa da irin shirye-shiryen da hukumar ta yi.
A nasa jawabin, babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana cewa, an samu nasarori da dama a kan shirye-shiryen gudanar da aikin hajjin shekarar 2024 a jihar.
Shugaban hukumar ya kara da cewa, hukumar ta kara wa’adin gudanar da lakcocin aikin hajji ga maniyyatan da ke fadin kananan hukumomi ashirin da bakwai na jihar.
Ya nanata kudurin gwamnatin jihar na tabbatar da jin dadin Alhazan Jigawa tun daga gida Najeriya har zuwa kasar Saudiyya.
Labbo ya yabawa NAHCON bisa ci gaba da bayar da goyon baya da hadin kai ga hukumar domin samun nasarar aikin Hajjin na bana.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, tawagar ta duba sashin amfani da na’ura mai kwakwalwa, da ayyukan da ake gudanarwa, tare da wasu gine-gine da aka gyara, da sauran kayayyakin zamani na hukumar.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar