Fasaha
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya koyawa sakamakon gwajin cancantar da gwamnatin jihar ta gudanar.
Sakamakon jarabawar ya nuna cewa daga cikin malamai 15,823 da suka zana jarabawar, 5,257 ne kawai suka samu nasara; 6,227 sukayi kasa da abin da ake buƙata, amma an yi la’akari da cewa idan suka horarwa zasu iya ci gaba da aikin; yayin da 4,339 aka gano ba su da horo kana ba zasu iya aikin ba.
Da yake kaddamar da shirin a kwalejin ilimi ta Waka Biu da ke karamar hukumar Biu, gwamna Babagana Zulum ya ce shirin zai ci gaba da daukar nauyin mutane 2,730 da suka amfana.
“Hakika, a ranar 19 ga Maris, 2024, gwamnati ta amince da ware Naira biliyan daya (N1 biliyan) don horar da malamai 2,730. Wadannan malaman za su yi horo ne a kwalejin ilimi ta Waka-Biu da kwalejin kimiyya da fasaha ta Umar Ibn Ibrahim Elkanemi Bama, domin gudanar da shirin na tsawon watanni uku ga masu cin gajiyar 1,884,” in ji Zulum.
A cewar Gwamnan, kimanin malamai 846 da ba su da takardar shedar kammala jami’a za su yi shirin kammala karatun samun shaidar horasda malamai ta NCE.
Ya ce horon ya fara ne da nufin inganta harkar ilimi a jihar, inda ya ce kowane mahaluki zai samu horon kyauta tare da biyan naira 30,000 duk wata a kan albashin da ya saba karba.
Shugaban kungiyar malamai ta Najeriya (NUT) reshen jihar Borno, Kwamared Zali Garba ya yabawa gwamna Zulum kan kawo sauyi a fannin ilimi.
Taron ya samu halartar Sanata mai wakiltar Kudancin Borno, Mohammed Ali Ndume; Mai Martaba Sarkin Biu, Mustapha Umar Aliyu II; ‘yan majalisar dokokin jihar Borno; Kwamishinan ilimi, kimiyya, fasaha da kirkire-kirkire, Lawan Abba Wakilbe da sauran manyan jami’an gwamnati.
Cov/Dauda/Wababe
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar