Connect with us

Labarai

Alhazai Za Su Biya Miliyan Bakwai Don Sauke Farali

Published

on

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta bukaci maniyyatan aikin Hajjin bana da su biya karin Nera Miliya Daya da Dubu Dari Tara kan kudaden da suka biya a baya.

Hakan na kunshe ne  cikin wata sanarwa da ta fito  da yammacin ranar Lahadi mai dauke da sa hannun mataimakiyar daraktar hulda da jama’a ta hukumar, Fatima Sanda Usara.

Fatima Usara ta kara da cewa  hukumar ta kuma bada wa’adin  ranar 29 ga Maris a matsayin ranar da za a kammala bada cikon kudin.

Ta ce hakan ya zama wajibi duba da yadda darajar Naira  ke faduwa a kowacce rana.

A baya dai hukumar ta tsayar da naira miliyan 4 da dubu dari 5 a matsayin kudin aikin Hajjin, kafin daga bisani ta kara naira dubu dari 4, ya zama naira miliyan hudu da dubu 9, sai kuma yanzu da ta sanar da karin kusan naira miliyan biyu.

Idan har wannan kari ya tabbata a yanzu, farashin kujerar aikin hajji zai tashi kan Naira miliyan 6 da dubu dari 9.

A watan Fabarairun da ya gabata ne Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Najeriya ta kayyade kusan naira miliyan biyar a matsayin kudin kuejrar hajjin bana.

 

Sai dai tun bayan lokacin, hukumar ta soma tababar kara wa maniyyatan kudi bisa dalilan faduwar darajar naira.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai30 mins ago

Fasinjoji 85 Sun Tsallake Rijiya Da Baya A Wani Hatsarin Jirgin Sama A Senegal

Wani jirgin sama samfurin 737 dauke da mutane 85 ya tsallake rijiya da baya a filin jiragen sama na Dakar,...

Labarai51 mins ago

Za a Dauki Mataki Kan Masu Cin Zarafin Yan Aikin Gida

A wani mataki na kare hakkin ‘yan aikin gida da ma kare iyayen gidan da ake yi wa aikin daga...

Labarai1 hour ago

Majalisar Dattawan ta Amince da Hukuncin Kisa ga Masu Safarar Kwaya

Majalisar dattawan Najeriya ta amince da ƙudurin dokar hukuncin kisa ga masu safarar miyagun ƙwayoyi a faɗin ƙasar, bayan ƙudurin...

Labarai1 hour ago

Kotu ta Bayar da Belin Hadi Sirika kan Naira Miliyan 100

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama na Nijeriya, Hadi Sirika ya musanta zargin aikata laifin almundahana da ya shafi kusan Naira...

Labarai1 day ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai1 day ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci2 days ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha2 days ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha2 days ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Mafi Shahara