Connect with us

Labarai

Fasinjoji 85 Sun Tsallake Rijiya Da Baya A Wani Hatsarin Jirgin Sama A Senegal

Published

on

Wani jirgin sama samfurin 737 dauke da mutane 85 ya tsallake rijiya da baya a filin jiragen sama na Dakar, da ke kasar Senegal, inda ya raunata mutane 10, kamar yadda hukumomin kasar suka tabbatar.

Mawakin kasar mai suna, Mali Cheick Siriman Sissoko wanda ya wallafa yadda lamarin ya auku a shafinsa na Facebook ya bayyana cewa, “Jirgin da muke ciki kawai ya kama da wuta,” yana mai cewa kururuwar mutane ta cika cikin jirgin a lokacin da al’amarin ya faru.

Ministan Sufuri El Malick Ndiaye ya ce jirgin Air Senegal ya nufi Bamako babban birnin kasar Mali da ke makwabtaka da kasar da yammacin Laraba, dauke  da fasinjoji 79 sai kuma matukan jirgi biyu da ma’aikatansa guda hudu.

Wadanda suka jikkata dai suna karbar kulawar likitoci a asibiti yanzu haka, yayin da sauran kuma aka kai su otel domin su huta.

Har yanzu dai babu wani cikakken bayani kan musababbin faruwar hatsarin jirgin.

Cibiyar Safety Network mai bin diddigin hadurran jiragen sama, ta wallafa hotunan yadda jirgin ya kafe a cikin wani fili mai dauke da ciyawa a shafinta na X.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Fasaha19 mins ago

Shugaban Kasa Ya Kaddamar Sabon Birnin Kasuwanci A Abuja

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da samarda wani da za a samar don gudanarda harkokin kasuwanci a cikinsa da...

Labarai50 mins ago

Kungiyar CAN Ta Rasa Mata Shida A Hadarin Mota A Taraba

An bayyana cewa wasu ’yan kungiyar mata ta kungiyar Kiristoci ta Najeriya (WOWICAN) su shida ne suka rasa rayukansu a...

Labarai1 hour ago

‘Yan Sakai Jihar Taraba Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Yi Garkuwa

Rundunar ‘yan banga ta Najeriya (VGN) reshen jihar Taraba ta yi nasarar ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa...

Ilimi1 hour ago

Talatar Nan Jirgin farko na Maniyatan jihar Kwara Zai Tashi

An dage tashin jirgin farko daga filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon na kasa da kasa na Ilorin don...

Labarai1 hour ago

HARIN MASALLACIN KANO: Obi Ya Ziyarci Wadanda suka Mutu

  Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya ziyarci wadanda kona masallacin Kano...

Labarai2 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi Ta Yi Kiran A Yiwa Mijinta Addu’a

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce addu’a ita ce ginshikin duk wani shugabanci mai nasara, don...

Labarai2 hours ago

Gwamnatin Kano Ta Rufe Asibitin Kwanar Ganduje A Kano

Gwamnatin jihar Kano, ta rufe tare asibitin Kwanar Ganduje dake unguwar Sharada Karamar Hukumar Kano Municipal.   Babban daraktan hukumar...

Labarai2 hours ago

Shugaban Iran Ebrahim Raisi Ya Rasu A Hatsarin Jirgi

Jami’an Iran sun ce Shugaba Ebrahim Raisi da ministan harkokin wajen ƙasar, Hossein Amir-Abdollahian sun rasu a wani hatsarin jirgin...

Labarai13 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Mafi Shahara