Labarai
Fasinjoji 85 Sun Tsallake Rijiya Da Baya A Wani Hatsarin Jirgin Sama A Senegal
Wani jirgin sama samfurin 737 dauke da mutane 85 ya tsallake rijiya da baya a filin jiragen sama na Dakar, da ke kasar Senegal, inda ya raunata mutane 10, kamar yadda hukumomin kasar suka tabbatar.
Mawakin kasar mai suna, Mali Cheick Siriman Sissoko wanda ya wallafa yadda lamarin ya auku a shafinsa na Facebook ya bayyana cewa, “Jirgin da muke ciki kawai ya kama da wuta,” yana mai cewa kururuwar mutane ta cika cikin jirgin a lokacin da al’amarin ya faru.
Ministan Sufuri El Malick Ndiaye ya ce jirgin Air Senegal ya nufi Bamako babban birnin kasar Mali da ke makwabtaka da kasar da yammacin Laraba, dauke da fasinjoji 79 sai kuma matukan jirgi biyu da ma’aikatansa guda hudu.
Wadanda suka jikkata dai suna karbar kulawar likitoci a asibiti yanzu haka, yayin da sauran kuma aka kai su otel domin su huta.
Har yanzu dai babu wani cikakken bayani kan musababbin faruwar hatsarin jirgin.
Cibiyar Safety Network mai bin diddigin hadurran jiragen sama, ta wallafa hotunan yadda jirgin ya kafe a cikin wani fili mai dauke da ciyawa a shafinta na X.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United