Connect with us

Labarai

Za a Dauki Mataki Kan Masu Cin Zarafin Yan Aikin Gida

Published

on

A wani mataki na kare hakkin ‘yan aikin gida da ma kare iyayen gidan da ake yi wa aikin daga fuskantar wata matsala daga kowanne bangare, majalisar dattawan Najeriya ta ce akwai bukatar samar da hukumar da zata rika tattara bayanan ‘yan aikin da kuma iyayen gidan na su.

Majalisar ta ce za a samar da hukumar ne domin tabbatar da kare ‘yan aiki wadanda a ko da yaushe suke fuskantar cin zarafi daga wajen iyayen gidansu.

Sannan kuma a kare iyayen gidan da a wasu lokutan ke fuskantar hadari daga masu yi musu aikin.

Matakin samar da hukumar da majalisar ke shirin yi ya biyo bayan wani kuduri da daya daga cikin ‘yan majalisar sanata Babangida Hussaini, ya gabatar a zauren majalisar wanda kuma ya samu cikakken goyon baya da kuma tsallake karatu na biyu a majalisar.

Sanata Babangida Hussaini, ya ce rashin dokar da zata rinka sanya ido da kuma bibiyar irin wadannan al’amura da ma sanya ido a kansu ya sa cin zarafi ‘yan aiki ya yawaita a Najeriya.

Sanatan ya ce irin hakan kuma kan janyo faruwar manyan laifuka kamar kisan kai a tsakanin ‘yan aiki da iyayen gidansu.

Babangida Hussaini ya ce,” A wasu lokuta zaka ga ba a biyan ‘yan aiki hakkinsu kamar yadda ya kamata, wadansu ana cin mutuncinsu inda wadansu ma har rasa rayukansu suke.”

Ya ce,” A bangaren masu daukar ‘yan aikin gidan kuma wato iyayen gida ke nan ana samun matsaloli kamar hada kai da masu aikin gida da wasu bata gari wajen sace sace ko kuma wani lokacinma a lalata yaran gida.”

” Wannan duk ya biyo bayan rashin tsari da ma sanya idanu ne.” in ji shi.

Kudurin dokar samar da hukumar dai zai gindaya wasu sharuda da sai an cika su kafin a dauki ‘yar aiki ko dan aiki, sannan dole shi ma mai daukar ‘yan aikin a samu bayanansa.

Sanata Babangida Hussaini, ya ce idan wannan kudurin ya zama doka to akwai dokar da za ayi wadda iyayen gida ba za su rinka cin mutuncin ‘yan aiki ba, sannan wajibi ne kuma a rinka kula da ci da sha da wajen kwanan ‘yan aiki.

Bashir M

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai26 mins ago

Muna Mika Sakon Ta’aziyar Mu Ga Al’ummar Iran – Tinibu

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya mika ta’aziyyarsa ga gwamnati da al’ummar Jamhuriyar Musulunci ta Iran bisa rasuwar shugaba Ebrahim Raisi;...

Fasaha2 hours ago

Gwamnan Kaduna Ya Kaddamar Da Sabbin Ajujuwa A Zaria

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya kaddamar da rukunin ajujuwa 18 a makarantun Basic Education guda biyu dake karamar hukumar...

Fasaha3 hours ago

Shugaban Kasa Ya Kaddamar Sabon Birnin Kasuwanci A Abuja

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da samarda wani da za a samar don gudanarda harkokin kasuwanci a cikinsa da...

Labarai3 hours ago

Kungiyar CAN Ta Rasa Mata Shida A Hadarin Mota A Taraba

An bayyana cewa wasu ’yan kungiyar mata ta kungiyar Kiristoci ta Najeriya (WOWICAN) su shida ne suka rasa rayukansu a...

Labarai3 hours ago

‘Yan Sakai Jihar Taraba Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Yi Garkuwa

Rundunar ‘yan banga ta Najeriya (VGN) reshen jihar Taraba ta yi nasarar ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa...

Ilimi4 hours ago

Talatar Nan Jirgin farko na Maniyatan jihar Kwara Zai Tashi

An dage tashin jirgin farko daga filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon na kasa da kasa na Ilorin don...

Labarai4 hours ago

HARIN MASALLACIN KANO: Obi Ya Ziyarci Wadanda Ke Asibiti

  Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya ziyarci wadanda kona masallacin Kano...

Labarai4 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi Ta Yi Kiran A Yiwa Mijinta Addu’a

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce addu’a ita ce ginshikin duk wani shugabanci mai nasara, don...

Labarai4 hours ago

Gwamnatin Kano Ta Rufe Asibitin Kwanar Ganduje A Kano

Gwamnatin jihar Kano, ta rufe tare asibitin Kwanar Ganduje dake unguwar Sharada Karamar Hukumar Kano Municipal.   Babban daraktan hukumar...

Labarai5 hours ago

Shugaban Iran Ebrahim Raisi Ya Rasu A Hatsarin Jirgi

Jami’an Iran sun ce Shugaba Ebrahim Raisi da ministan harkokin wajen ƙasar, Hossein Amir-Abdollahian sun rasu a wani hatsarin jirgin...

Mafi Shahara