Connect with us

Labarai

Senegal Ta Kama Tan Guda Na Hodar Ibilis

Published

on

Hukumar Kwastam ta Senegal ta ce ta kwato fiye da tan guda na hodar ibilis a kudu maso gabashin kasar, inda ta bayyana shi a matsayin kamu mafi girma da aka taba yi na jigilar hodar iblis a kan hanyar kasa a yammacin Afirka.

Hukumar ce an kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram dubu daya da dari daya da talatin da bakwai da digo shidda  a ranar Lahadin da ta gabata a garin Kidira, wacce ta kiyasta kudinsa zai kai sama da CFA biliyan 90, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 146.

Sanarwar ta ce, wannan shi ne kamu mafi girma na hodar iblis ta hanyar kasa da aka taba samu a Senegal.

Hukumar ta ce an boye hodar ne a cikin fakiti-fakiti kuma an sanya shi a cikin jakunkuna a wata mota mai daukar kayan sanyi da ta fito daga wata kasa mai makwabtaka da Senegal, wadda ba ta bayyana sunan kasar ba.

Kasar Senegal dai tana iyaka da kasashen Guinea da Gambia da Guinea Bissau da Mauritania da kuma Mali, kasashen da aka san su ne wuraren safarar magungunan da ake samarwa a Amurka ta Kudu akan hanyarsu ta zuwa Turai.

Yammaci da tsakiyar Afirka ya zama yankin da ake yawan amfani da shi, a cewar ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai yaki da miyagun kwayoyi da laifuffuka.

A watan Oktoban 2022, an kama kilogiram 300 na hodar iblis daga wata motar daukar kaya masu sanyi da ta taho daga Mali.

Haka kuma Rundunar sojin Senegal a watan Nuwamban bara, ta ce ta gano kusan tan uku na hodar iblis daga wani jirgin ruwa a gabar teku.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai7 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai7 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai20 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara