Labarai
‘Yan Sanda Sun Kama Tirelar Sata Makare Da Kaya A Bauchi

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, ta cafke wani da ake zargin barawo ne da ya sace wata tirela dauke da tan 35 na man gyada da darajarsa ta kai kimanin Naira miliyan 30.
Rundunar ta samu rahoton sace tirelar da aka ajiye a yankin Maraban Jos a Jihar Kaduna a ranar 12 ga watan Afrilun 2024.
Kakakin rundunar, SP Ahmed Wakil, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ya ce motar da aka sace mai lamba DAF CF 85, ta fito ne daga Umuahia a Jihar Abiya.
SP Wakil, ya ce bincike ya nuna cewa direban motar ya tsaya a Maraban Jos don yin wanka amma yana dawowa ya tarar an sace ta.
Kakakin ya ce rundunar ta samu damar kwato kaya masu yawa a cikin tirelar.
-
Labarai5 days ago
Max Air Zai Yi Jigilar Alhazan Jigawa A Ranakun 20 Da 21 Ga Watan Mayu
-
Labarai6 days ago
NUJ Ta Kafa Kwamitin Ladabtarwa A Jigawa
-
Labarai6 days ago
Builder Muhammad Uba Ya Sami Lambar Yabo Ta Rootswatch
-
Labarai4 days ago
Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa
-
Kasuwanci7 days ago
Majalisar Dokokin Kaduna Ta Amince Da Kudirin Dokar Hukumar Kula Da Manyan Makarantun Sakandire
-
Kasuwanci7 days ago
Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Da Jirgin Alhazan Kano Na Farko
-
Fasaha7 days ago
Gwamnatin Zamfara Ta Bukaci A Kiyaye Makarantun Da Aka Gyara.
-
Labarai7 days ago
Kashi Na Biyu Na Maniyyata 415 Daga Jihar Kwara Sun Tashi Zuwa Kasar Saudiyya