Connect with us

Labarai

An Nada Sarkin Dass A Matsayin Amirul Hajji Na Jihar Bauchi

Published

on

Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed na jihar Bauchi ya amince da nadin Sarkin Dass Alhaji Usman Bilyaminu Othman, a matsayin Amirul Hajji na Jahar don gudanar da aikin Hajjin 2024 a kasa mai tsarki.

Wasikar nadin mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Barista Ibrahim Mohammed Kasim na nuni da cewa nadin nasa tare da wasu fitattun ‘yan jihar 13, an yi sa ne bisa jajircewar su da sadaukar da kai, da kiyaye dokokin  Allah Madaukakin Sarki.

Gwamna Bala Mohammed ya bayyana kwarin guiwar tawagar da aka nada, inda ya jjaddada cewa yana da yakimin za su yi aiki yadda yakamata.Ya nanata kudurin gwamnatin jihar na tallafawa alhazai da kuma tabbatar da jin dadin su a tsawon tafiyarsu.

Sauran membobin tawagar ta Amirul Hajj sun hada da mataimakin shugaban  majalisar jihar Honarabul  Jamilu Umar Dahiru a matsayin mataimakin Amirul Hajj,da mai shari’a Rabi Talatu Umar, Babbar Alkalin Jihar Bauchi, da
Khadi Umar Ahmed Liman, da Honarabul Yakubu Ibrahim Hamza, da kuma Honarabul.

Sauran sun hada da Alhaji Ibrahim Y.M Baba Hakimin Yelwan Duguri, da Galadiman Bauchi Surv. Ibrahim Saidu Jahun, da Alhaji Yayanuwa Zainabari
da  Sheikh Zubairu A. Madaki, da kuma Sheikh Salisu Sulaiman Ningi.

Har ila yau akwai Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi, da Malam Ahmad Inuwa Na’ibi, da kuma Muhammad Haruna Barde a matsayin sakataren tawagar.

Tawagar za ta yi aiki tare da hukumomin da abin ya shafa da suka hada da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jiha, da Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) da kuma Gwamnatin Saudiyya, domin tabbatar da ganin an samu nasarar gudanar da aikin hajjin bana ga daukacin alhazan Jihar Bauchi.

Gwamnan ya bukaci tawagar da aka nada da ta bada himma wajen gudanar da ayyukanta, tare da tabbatar da bin gaskiya da  adalci.

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai6 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai7 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai20 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara