Labarai
Gwamnatin Bauchi Za Ta Biya Kashi 50 Na Cikon Kudin Aikin Hajji
Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad ya amince da biyan kashi hamsin bisa dari na cikon kudaden aikin Hajjin 2024 ga Alhazan jihar.
Hakan ya biyo bayan sanarwar da Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta yi, na karin Nera Miliyan daya da dubu dari tara da goma sha takwas, kan Nera Miliyan hudu da dubu dari shida da suka biya a baya.
A don haka ne gwamnatin jihar Bauchi karkashin jagorancin Gwamna Bala Muhammad ta kudiri aniyar bada tallafi ga Alhazan jihar, inda za a biya wa kowani maniyyaci Nera dubu dari tara da hamsin da tara.
Gwamnan ya amince da a biya Nera Miliyan dubu biyu da dari daya da casa’in da shidda domin tallafawa maniyyatan jihar su dubu biyu da dari biyu da casa’in.
Safiyah Abdulkadir
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai6 days ago
An Kashe Makiyaya 2 Da Shanu 150 A Sabon Hari A Filato