Connect with us

Labarai

Gwamnatina Ta Gaji Bashin $587m Da N85bn – Gwamna Uba Sani

Published

on

 

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce gwamnatinsa ta gaji bashin dala miliyan 587 da bashin Naira biliyan 85 da kuma ayyukan kwangila 115 daga gwamnatin Nasir El-Rufai.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne a Kaduna a ranar Asabar yayin da yake jawabi a wajen wani taro, inda ya ce dimbin bashin da ake bin jihar na laƙume abin da jihar ke samu.

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta ware Naira biliyan bakwai daga cikin Naira billiyan 10 da Gwamnatin Tarayya ta ware mata a watan Maris, domin biyan bashi.

Gwamna Sani ya koka kan tashin farashin canji, wanda ya ce jihar na biyan kusan ninki uku na bashin da gwamnatin baya ta karbo.

Ya Kuma koka da yadda gwamnatin El-Rufai ta bar wa jihar biliyan uku kacal a asusun jihar, wanda ya gaza biyan albashin ma’aikata da ake biya na Naira biliyan 5.2 a duk wata.

Gwamna Sani, ya ce gwamnatinsa ba ta ci bashin ko sisi ba tun bayan wata tara da ya hau mulki, duk da dimbin bashin da ya gada.

“Mun yi nazari cikin tsanaki kan halin da muke ciki. Ina sanar da ku cewa duk da dimbin bashin da muka gada, har zuwa yanzu ba mu ciyo bashin ko kobo ba,” in ji shi.

Gwamnan ya kara da cewa muhimman abubuwan da gwamnatinsa ta sa a gaba sun hada da tsaro, samar da gidaje, ilimi, kiwon lafiya, da tallafa wa masu kananan sana’o’i.

Ya ce gwamnatinsa za ta kuma mayar da hankali wajen samar da ci gaba ta hanyar saka hannun jari, inganta tattalin arziki da samar da gidaje masu sauki.

Una Sani, ya bayyana wasu muhimman abubuwan da gwamnatinsa ta sa a gaba a 2024 da suka haɗa da tsaro, samar da ababen more rayuwa, bunkasa ilimi, samar da gidaje da ci gaban birane da dai sauransu.

A nasa jawabin, tsohon Babban Hafsan Hafsoshi, Janar Martin Luther Agwai (mai ritaya), ya bukaci a ɓullo da hanyoyin magance matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta, inda ya ce idan ba a samu zaman lafiya da tsaro ba, ba za a iya samun ci gaban da jihar ke muradi ba.

Ya yaba wa gwamnan kan yadda ya rage hanyoyin da kuɗaɗen tafiyar da gwamnati ke zurarewa.

Ya bukaci al’ummar jihar da su guji nuna bambancin siyasa, addini ko kabilanci tare da mara wa gwamnatin jihar baya domin shawo kan kalubalen bashi da ta ke fuskanta.

Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamali, ya yi wa gwamnatin fatan alheri duk da kalubalen da ta ke fuskanta.

Ya kuma kara da cewa gwamnan yana da gogewar da zai inganta tattalin arzikin jihar domin samun ci gaba.

 

 

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara